< John 2 >

1 And, on the third day, a marriage, took place, in Cana, of Galilee; and the mother of Jesus was there, —
Bayan kwana uku, akwai aure a Kana ta Galili, mahaifiyar Yesu kuma tana wurin.
2 and Jesus also was invited, with his disciples, unto the marriage.
An gayyaci Yesu da almajiransa zuwa auren.
3 And, wine falling short, the mother of Jesus saith unto him—Wine, have they none!
Da ruwan inabin ya kare, maihafiyar Yasu tace masa, “basu da ruwan inabi.”
4 And Jesus saith unto her—What part can I take with thee, O woman? Not yet, hath come, mine hour.
Yesu yace mata, “Mace, me yasa kika zo wurina? Lokaci na bai yi ba tukuna”.
5 His mother saith unto them who are ministering—Whatsoever he may say to you, do!
Maihafiyarsa tace wa ma'aikatan, “Ku yi duk abin da yace maku.”
6 Now there were there, six stone water-vessels, placed, according to the purification of the Jews; holding each, two or three measures.
To akwai randunan ruwa na dutse guda shidda a wurin wadanda Yahudawa ke amfani da su domin al'adansu na tsarkakewa, kowace zata iya daukar durom guda.
7 Jesus saith unto them—Fill the vessels with water. And they filled them up to the brim.
Yesu yace masu, “Cika randunan da ruwa”. Sai suka cika randunan makil.
8 And he saith unto them—Draw out now, and be bearing unto the master of the feast. And they bare.
Sai yace wa ma'aikatan, “Ku diba daga ciki ku kai wa shugaban biki.” Sai suka yi hakannan.
9 And, when the master of the feast had tasted the water, now made, wine, and knew not whence it was, —though, they who were ministering, knew, even they who had drawn out the water, the master accosteth the bridegroom,
Shugaban bikin ya dandana ruwan da ya zama ruwan inabin, amma bai san inda ya fito ba (amma ma'aikatan wadanda suka jawo ruwan sun sani). Sai ya kira ango
10 and saith unto him—Every man, first the good wine, setteth out; and, when they had been well-supplied, the inferior: —Thou, hast kept the good wine until, even now.
yace masa, “Kowane mutum yakan raba ruwan inabi mai kyau da farko, kafin mai arhar bayan an shanye mai kyaun. Amma kai ka ajiye mai kyaun sai yanzu.”
11 This, beginning of his signs, did Jesus, in Cana of Galilee, and manifested his glory; and his disciples believed on him.
Wannan alama ta farko ce da Yesu yayi a Kana ta Galili, ya kuma bayyana daukakarsa, almajiransa kuma suka gaskata da shi.
12 After this, he came down into Capernaum, —he, and his mother and brethren, and his disciples; and, there, they abode, not many days.
Bayan wannan, Yesu, da mahaifiyarsa, da 'yan'uwansa da almajiransa suka tafi Kafarnahum, kuma suka zauna can wasu 'yan kwanaki.
13 And, near, was the passover of the Jews; and, Jesus, went up unto Jerusalem.
To idin ketarewa na Yahudawa ya kusato, Yesu kuwa ya wuce zuwa Urushalima.
14 And he found, in the temple, them that were selling oxen and sheep and doves, also the money-changers sitting.
Ya iske wadanda suke sayar da shanu da tumaki da tantabaru, masu canjin kudi kuma na zaune a wurin.
15 And, making a scourge out of rushes, all of them, thrust he forth out of the temple, both the sheep and the oxen; and, the money-changers’ small coins, poured he forth, and, the tables, he overturned;
Sai yayi tsumingiya da igiyoyi ya kore su duka daga cikin haikalin, duk da tumakin da shanun. Sai ya watsar da sulallan masu canjin kudin ya birkitar da teburansu.
16 and unto them who were selling, the doves, he said—Take these things hence! Be not making, the house of my Father, a house of merchandise.
Yace wa masu sayar da tantabaru, “Ku fitar da wadannan abubuwa daga nan. Ku daina maida gidan Ubana wurin kasuwanci.”
17 His disciples remembered that it was written—The zeal of thy house, eateth me up.
Almajiransa suka tuna a rubuce yake, “Himma domin gidanka za ta cinye ni.”
18 The Jews therefore answered, and said unto him, What sign, dost thou point out to us, in that, these things, thou doest?
Sai shugabannin Yahudawa suka amsa suka ce masa, “Wace alama za ka nuna mana, da shike kana yin wadannan abubuwan?”
19 Jesus answered, and said unto them—Take down this shrine, and, in three days, will I raise it.
Yesu ya amsa, “Ku rushe wannan haikali, kuma a cikin kwana uku zan gina shi.”
20 The Jews, therefore, said—In forty and six years, was this shrine built. And, thou, in three days, wilt raise it!
Sai shugabanin Yahudawa suka ce, “An dauki shekaru arba'in da shidda kamin a gama gina wannan haikalin, za ka dau kwanaki uku kadai wajen gina shi?”
21 But, he, was speaking concerning the shrine of his body.
Amma yana nufin haikali na jikinsa ne.
22 When, therefore, he had been raised from among the dead, his disciples remembered, that, this, he had been saying; and they believed in the Scripture, and in the word which Jesus had spoken.
Bayan da aka tashe shi daga matattu, sai almajiransa suka tuna ya fadi haka, suka kuma ba da gaskiya ga nassi da wannan kalami da Yesu ya fada.
23 Now, when he was in Jerusalem, during the passover, during the feast, many, believed on his name, viewing his signs which he was doing.
Kuma, da yana Urushalima a idin ketarewa, a lokacin idin, mutane da yawa suka gaskata ga sunansa, sa'adda suka ga alamun da ya yi.
24 Jesus himself, however, was not trusting himself unto them, by reason of his understanding them all,
Amma Yesu bai yadda da su ba domin ya san su duka,
25 and because he had, no need, that anyone should bear witness concerning man; for, he, understood what was in man.
saboda baya bukatar wani ya shaida masa game da mutum, domin ya san abinda ke cikin sa.

< John 2 >