< Deuteronomy 18 >

1 Neither the priests the Levites [nor] any of the tribe of Levi, shall have either portion or inheritance with Israel, —the altar-flames of Yahweh and his inheritance, shall they eat.
Firistocin da suke Lawiyawa, tabbatacce dukan kabilar Lawi, ba za su sami rabo ko gādo tare da Isra’ila ba. Za su yi rayuwa a kan hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta ne, gama wannan ne gādonsu.
2 But inheritance, shall he not have, in the midst of his brethren, —Yahweh, is his inheritance, as he spake unto him.
Ba za su sami gādo a cikin’yan’uwansu ba; Ubangiji ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
3 This, therefore shall be the due of the priests from the people from them who offer the sacrifice whether ox or lamb, —there shall be given unto the priest, the shoulder and the two cheeks and the maw:
To, ga rabon da jama’a za su ba firistoci daga hadayun da suka miƙa ta bijimi ne, ko ta tunkiya ce; sai su ba firistoci kafaɗar, kumatun, da kuma kayan cikin.
4 the firstfruit of thy corn thy new wine and thine oil and the first of the fleece of thy flock, shalt thou give unto him.
Za ku ba su nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabinku, da manku, da kuma gashi na fari daga askin da kuka yi na tumakinku.
5 For of him, hath Yahweh thy God made choice out of all thy tribes, —to stand to minister in the name of Yahweh of him and his sons all the days.
Gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su da zuriyarsu daga cikin dukan kabilanku don su tsaya su yi hidima a cikin sunan Ubangiji har abada.
6 And when the Levite shall come in out of any of thy gates out of any part of Israel, where he is sojourning, —yea shall come in with all the desire of his soul, into the place which Yahweh shall choose,
Idan Balawe ya tashi daga wani garinku, wurin da yake da zama a Isra’ila, ya tafi a wurin da Ubangiji ya zaɓa, zai iya dawo a duk lokacin da ya ga dama.
7 then may he minister in the name of Yahweh his God, —like any of his brethren the Levites who are standing there before Yahweh.
Zai iya yin hidima a cikin sunan Ubangiji Allahnsa kamar dukan sauran’yan’uwansa Lawiyawa waɗanda suke hidima a can, a gaban Ubangiji.
8 Portion for portion, shall they eat, —apart from his possessions upon his patrimony.
Zai sami rabo daidai da sauran, ko da yake ya karɓi kuɗin mallaka na iyali da ya sayar.
9 When thou art coming into the land which Yahweh thy God is giving unto thee, thou shalt not learn to do according to the abominable doings of those nations.
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku kwaikwayi hanyoyin banƙyama na al’ummai da suke can.
10 There shall not be found in thy midst—One who causeth his son or his daughter to pass through fire, —Or who useth divination, hidden arts or enchantments Or who muttereth incantations;
Kada a sami wani a cikinku da ya miƙa ɗansa, ko’yarsa a wuta, ko a sami mai duba, ko mai maita, ko mai fassara gaibi, ko mai sihiri,
11 Or who bindeth with spells, —Or who asketh of a familiar spirit or an oracle, Or who seeketh unto the dead.
ko boka, ko mabiya, ko maye, ko mai sha’ani da matattu.
12 For, an abomination unto Yahweh, is everyone who doeth these things, —and on account of these abominations, is Yahweh thy God dispossessing them from before thee.
Duk wanda yake yin waɗannan abubuwa, shi abin ƙyama ne ga Ubangiji, saboda waɗannan abubuwa banƙyama ne kuwa Ubangiji Allahnku ya kori waɗancan al’ummai kafin ku.
13 Blameless, shalt thou be with, Yahweh thy God;
Dole ku zama marasa zargi a gaban Ubangiji Allahnku.
14 for, these nations whom thou art dispossessing, unto them who use hidden arts and unto diviners, do hearken, but as for thee, not so, doth Yahweh thy God suffer thee.
Al’ummai da za ku kora sukan saurari waɗannan masu maita, ko masu duba. Amma ku, Ubangiji Allahnku bai yarda muku ku yi haka ba.
15 A prophet out of thy midst of thy brethren like unto me, will Yahweh thy God, raise up unto thee—unto him, shall ye hearken:
Ubangiji Allahnku zai tayar muku da wani annabi kamar ni daga cikin’yan’uwanku. Dole ku saurare shi.
16 according to all which thou didst ask of Yahweh thy God, in Horeb, in the day of the convocation saying, —Let me no further hearken unto the voice of Yahweh my God, and this great fire, let me not see any more lest I die.
Gama abin da kuka nema daga Ubangiji Allahnku ke nan a Horeb, a ranar taro, sa’ad da kuka ce, “Kada ka bari mu ji muryar Ubangiji Allahnmu, ko mu ƙara ganin wuta mai girma, in ba haka ba, za mu mutu.”
17 And Yahweh said unto me: They have well said what they have spoken.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Abin da suka faɗa yana da kyau.
18 A prophet, will I raise up unto them, out of the midst of their brethren, like unto thee, —and I will put my words in his mouth, so shall he speak unto them whatsoever I shall command him.
Zan tayar musu da wani annabi kamar ka daga cikin’yan’uwansu; zan sa kalmomina a cikin bakinsa, zai kuma faɗa musu kome da na umarce shi.
19 And it shall come to pass, that, the man who will not hearken unto my words which he shall speak in my name, I, myself will require it of him.
Duk wanda bai saurari kalmomina da annabin nan yake magana da sunana ba, ni kaina zan nemi hakki a kan mutumin.
20 Howbeit the prophet who shall presume to speak a word in my name which I have not commanded him to speak, or who shall speak in the name of other gods, that prophet shall die.
Amma duk annabin da ya ɗauka cewa yana magana da sunana a kan wani abin da ban umarce shi ya faɗa ba, ko kuwa wani annabin da ya yi magana da sunan waɗansu alloli, dole a kashe shi.”
21 And, when thou shalt say in thy heart, —In what manner shall we know the word which Yahweh hath not spoken!?,
Mai yiwuwa ku ce wa kanku, “Yaya za mu san cewa wannan saƙo ba Ubangiji ne ya faɗa ba?”
22 When the prophet shall speak in the name of Yahweh and the word shall not come to pass, neither shall come in, that, is the word which Yahweh, hath not spoken, —presumptuously, hath the prophet spoken it, thou shall not be in dread of him.
In abin da annabin ya furta da sunan Ubangiji bai faru ba, ko bai zama gaskiya ba, saƙo ne da Ubangiji bai faɗa ba ke nan. Wannan annabi ya yi rashin hankali ne kawai. Kada ku ji tsoronsa.

< Deuteronomy 18 >