< Deuteronomy 17 >

1 Thou shalt not sacrifice unto Yahweh thy God a bullock or a sheep wherein is a blemish, any unseemly thing: for an abomination unto Yahweh thy God, it would be.
Kada ku miƙa wa Ubangiji Allahnku, saniya ko tunkiyar da take da wani lahani, ko naƙasa a cikinta, gama wannan zai zama abar ƙyama gare shi.
2 When there shall be found in thy midst, within any of thy gates, which Yahweh thy God is giving unto thee, man or woman who doeth the thing which is wicked in the eyes of Yahweh thy God by transgressing his covenant;
In an sami wani namiji ko ta mace mai zama a cikinku, a ɗaya daga biranen da Ubangiji ya ba ku yana aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnku ta wurin karya alkawarinsa,
3 yea hath gone, and served other gods, and bowed down unto them, —whether unto the sun or unto the moon or unto any of the host of the heavens which I have not commanded;
wanda ya saba wa umarnina, har ya yi sujada ga waɗansu alloli, yana rusuna musu, ko ga rana, ko ga wata, ko kuwa ga taurarin sama,
4 and it shall be told thee and thou shalt hear, —and shalt enquire diligently, and lo! true—certain, is the report, this abominable thing hath been done in Israel,
in kuwa aka faɗa muku wannan, to, dole a bincika sosai. In kuwa gaskiya ne, aka kuma tabbatar cewa wannan abin ƙyama ya faru a cikin Isra’ila,
5 then shalt thou bring forth that man or that woman who hath done this wicked thing, within thy gates—the man, or the woman, —and shalt stone them with stones that they die.
sai a ɗauki namijin, ko ta mace wanda ya aikata wannan mugun abu zuwa ƙofar birni, a jajjefe wannan mutum sai ya mutu.
6 At the mouth of two witnesses or three witnesses, shall he that is to die be put to death, —he shall not be put to death at the mouth of one witness.
Bisa ga shaidar mutum biyu ko uku, za a iya kashe mutum, amma ba za a iya kashe mutum bisa ga shaida mutum guda ba.
7 The hand of the witnesses, shall be upon him first to put him to death, and the hand of all the people, afterwards, —so shalt thou consume the wicked thing out of thy midst.
Hannuwan shaidun ne za su zama na farko a kisan wanda ake zargin, sa’an nan hannuwan dukan mutane. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
8 When any matter of judgment, shall be too difficult for thee—between blood and blood between plea and plea or between stroke and stroke, matters of contention within thy gates, then shalt thou arise and go up unto the place which Yahweh thy God shall choose;
In aka kawo ƙarar da yake da wuya sosai ga alƙali a kotunanku, ko wadda aka zub da jini ne, ko ta faɗa ce, ko kuwa ta wadda aka ci mutunci ce, ku kai su wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa.
9 and shalt come in unto the priests the Levites, and unto the judge who shall be in those days, —and shalt enquire and they shall declare unto thee, the sentence of judgment;
Ku je wurin firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, ga kuma alƙalin wanda yake mulki a lokacin. Ku bincika daga gare su, za su kuwa ba da hukunci.
10 and thou shalt do according to the sentence which they shall declare unto thee, out of that place, which Yahweh, shall choose, —yea thou shalt observe to do according to all which they shall direct thee:
Dole ku aikata hukuncin da suka yi a wurin da Ubangiji zai zaɓa. Ku lura fa, ku aikata kome da suka faɗa muku.
11 according to the direction wherewith they direct thee and after the judgment which they shall announce to thee, shalt thou do, —thou shalt not turn aside from the sentence which they shall declare unto thee to the right hand or to the left.
Ku yi bisa ga dokar da suka koyar muku da kuma hukuncin da suka yi muku. Kada ku juya daga abin da suka faɗa muku, ko zuwa dama, ko zuwa hagu.
12 And, the man who shall do presumptuously by not hearkening unto the priest that standeth to minister there to Yahweh thy God, or unto the judge, that man shall die, and so shalt thou consume the wicked thing out of Israel.
Duk mutumin da ya yi rashin hankali wa alƙali, ko ga firist wanda yake aiki a nan wa Ubangiji Allahnku, dole a kashe shi. Dole ku fid da mugu daga Isra’ila.
13 And, all the people, shall hear and fear, —and shall not act presumptuously any more.
Dukan mutane kuwa za su ji, su kuma ji tsoro, ba kuwa za su ƙara yin rashin hankali kuma ba.
14 When thou shalt enter into the land which Yahweh thy God is giving unto thee, and shalt possess it and dwell therein, —and shalt say—I will set over me a king, like all the nations that are round about me,
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta, sai kuka ce, “Bari mu naɗa sarki a kanmu kamar sauran al’umman da suke kewaye da mu,”
15 thou shalt, set, over thee as king, him whom Yahweh thy God shall choose, —out of the midst of thy brethren, shalt thou set over thee a king, thou mayest not appoint over thee a man that is a foreigner, who is not thy brother.
ku tabbata kun naɗa sarki a kanku wanda Ubangiji Allahnku ya zaɓa ne. Dole yă zama daga cikin’yan’uwanku. Kada ku sa baƙo a kanku, wanda ba mutumin Isra’ila ɗan’uwanku ba.
16 Moreover he shall not multiply to himself horses, neither shall he cause the people to return to Egypt that he may multiply horses, —when, Yahweh, hath said unto you, Ye shall not again return this way any more.
Sarkin, ba zai nemi dawakai da yawa wa kansa ba, ko yă sa mutane su koma Masar don su sami ƙarin dawakai ba, gama Ubangiji ya faɗa muku, “Ba za ku ƙara koma wancan hanya kuma ba.”
17 Neither shall he multiply to himself wives, that his heart turn not aside, —nor silver and gold, shall he multiply to himself greatly.
Sarkin ba zai auri mata masu yawa ba, in ba haka ba zuciyarsa za tă karkata. Ba zai tara azurfa da zinariya da yawa ba.
18 But it shall be when he sitteth upon the throne of his kingdom, then shall he write for himself a copy of this law upon a scroll, out of that which is before the priests the Levites:
Sa’ad da ya hau kursiyin mulkinsa, sai yă rubuta wa kansa a littafin kofin wannan doka da aka ɗauka daga na firistoci, waɗanda suke Lawiyawa.
19 so shall it be with him, and he shall read therein all the days of his life, —that he may learn to revere Yahweh his God, to observe all the words of this law and these statutes to do them:
Zai kasance tare da shi, zai kuma karanta shi dukan kwanakin ransa, saboda yă koyi girmama Ubangiji Allahnsa, yă kuma bi dukan kalmomin wannan doka da kuma waɗannan ƙa’idodi a hankali
20 that his heart may not be lifted up above his brethren, and he may not turn aside from the commandment to the right hand or to the left, —that he may prolong his days over his kingdom—he and his sons, in the midst of Israel.
don kada yă ɗauki kansa ya fi’yan’uwansa, yă kuma juya daga dokar zuwa dama, ko zuwa hagu. Sa’an nan shi da kuma zuriyarsa za su daɗe suna mulki a Isra’ila.

< Deuteronomy 17 >