< 2 Timothy 1 >

1 Paul, an apostle of Meshikha Yeshua through the will of God, according to the promise of the life which is in Meshikha Yeshua,
Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, bisa ga alkawarin rai da ke cikin Almasihu Yesu,
2 to Timothy, my beloved child: Grace, mercy, and peace, from God the Father and Meshikha Yeshua our Lord.
zuwa ga Timoti, kaunataccen da: Alheri, jinkai, da salama daga Allah Uba da Almasihu Yesu Ubangijinmu.
3 I thank God, whom I serve as my forefathers did, with a pure conscience. How unceasing is my memory of you in my petitions, night and day
Na gode wa Allah, wanda na ke bautawa tun daga kakannina, da lamiri mai tsabta, sa'adda na ke tuna wa da kai cikin addu'o'ina koyaushe (dare da rana).
4 longing to see you, remembering your tears, that I may be filled with joy;
Sa'adda na tuna da hawayenka, na yi marmarin ganinka, saboda in cika da farin ciki.
5 having been reminded of the unfeigned faith that is in you; which lived first in your grandmother Lois, and your mother Euniki, and, I am persuaded, in you also.
An tunashshe ni game da sahihiyar bangaskiyarka, wadda ta samo asali daga kakarka Loyis da mahaifiyarka Afiniki. Na kuma tabbata ta na zaune a cikinka.
6 For this cause, I remind you that you should stir up the gift of God which is in you through the laying on of my hands.
Wannan shine dalilin da ni ke tunashshe ka cewa ka sake rura baiwar Allah da ke cikinka wadda ka samu sa'adda na dibiya maka hannuwana.
7 For God did not give us a spirit of fear, but of power and love and of a sound mind.
Domin Allah bai ba mu ruhun tsoro ba, amma na iko da kauna da kamun kai.
8 Therefore do not be ashamed of the testimony of our Lord, nor of me his prisoner; but endure hardship for the Good News according to the power of God,
Saboda haka kada ka ji kunyar shaida ga me da Ubangijinmu, ko ni, Bulus, daurarrensa. Maimakon haka, ka zama a shirye ka sha wahala domin bishara bisa ga ikon Allah.
9 who saved us and called us with a holy calling, not according to our works, but according to his own purpose and grace, which was given to us in Meshikha Yeshua before time began, (aiōnios g166)
Allah ne ya cecemu kuma ya kira mu da kira mai tsarki. Ya yi wannan, ba ta wurin ayyukanmu ba, amma ta wurin shirinsa da alherinsa. Ya ba mu wadannan abubuwan a cikin Almasihu Yesu kafin farkon zamanai. (aiōnios g166)
10 but has now been revealed by the appearing of our Savior, Meshikha Yeshua, who abolished death, and brought life and immortality to light through the Good News.
Amma yanzu an bayyana ceton Allah ta wurin bayyanuwar mai cetonmu Almasihu Yesu. Almasihu ne ya kawo karshen mutuwa ya kuma kawo rai marar karshe da ya bayyana ta wurin bishara.
11 For this, I was appointed a preacher, an apostle, and a teacher.
Domin wannan, an zabe ni mai wa'azi, manzo da mallami zuwa ga al'ummai.
12 For this cause I also suffer these things. Yet I am not ashamed, for I know him whom I have believed, and I am persuaded that he is able to guard that which I have committed to him against that day.
Domin wannan dalili na ke shan wahalar wadannan abubuwa. Amma ban ji kunya ba, domin na san shi, wanda na gaskanta. Na sakankance zai iya adana abinda na mika masa har zuwa ranan nan.
13 Hold the pattern of sound words which you have heard from me, in faith and love which is in Meshikha Yeshua.
Ka adana misalin amintattun sakwanni da ka ji daga gare ni, ta wurin bangaskiya da kauna da ke cikin Almasihu Yesu.
14 That good thing which was committed to you, guard through the Rukha d'Qudsha who dwells in us.
Abu mai kyau da Allah ya danka maka, ka tsare shi ta wurin Ruhu Mai Tsarki, da ke zaune a cikinmu.
15 This you know, that all who are in Asia turned away from me; of whom are Phygelus and Hermogenes.
Ka dai sani, dukkan wadanda su ke zama a Asiya sun juya mani baya. A cikin kungiyar akwai Fijalas da Harmajanas.
16 May the Lord grant mercy to the house of Onesiphorus, for he often refreshed me, and was not ashamed of my chain,
Bari Ubangiji ya yi wa iyalin Onisifaras jinkai, domin ya na yawan yi mani hidima, kuma ba ya jin kunyar sarkata.
17 but when he was in Rome, he sought me diligently, and found me
Maimakon haka, sa'adda ya ke a Roma, ya neme ni da kokarin gaske, ya kuma same ni.
18 (the Lord grant to him to find the Lord's mercy in that day); and in how many things he served at Ephesus, you know very well.
Bari Ubangiji ya sa, ya sami jinkai daga gare shi a wannan rana. Dukkan hanyoyin da ya taimake ni a kasar Afisa, kun sani sarai.

< 2 Timothy 1 >