< 1 Timothy 6 >

1 Let as many as are slaves under the yoke count their own masters worthy of all honor, that the name of God and the doctrine not be blasphemed.
Bari duk wadanda ke bayi a karkashin karkiya su ga iyayengijinsu sun cancanci dukan daraja. Su yi haka domin kada a sabawa sunan Allah da koyarwarsa.
2 Those who have believing masters, let them not despise them, because they are brothers, but rather let them serve them, because those who partake of the benefit are believing and beloved. Teach and exhort these things.
Bayin da suke da iyayengiji da ke masu ba da gaskiya kada su rena su saboda su 'yan'uwa ne. A maimakon haka, su yi masu hidima da kwazo. Gama iyayengijin da suke cin ribar aikinsu masu bi ne, kaunattatu kuma. Ka koyar ka kuma bayyana wadannan abubuwa.
3 If anyone teaches a different doctrine, and does not consent to sound words, the words of our Lord Yeshua Meshikha, and to the doctrine which is according to godliness,
Idan ya kasance wani na koyar da wani abu dabam bai kuma yarda da amintaciyar koyarwa ba, wato maganar Ubangijinmu Yesu Almasihu. Alal misali ba su amince da koyarwa da ke kai ga Allahntaka ba.
4 he is conceited, knowing nothing, but obsessed with arguments, disputes, and word battles, from which come envy, strife, reviling, evil suspicions,
Wannan mutum mai girman kai ne, kuma bai san komai ba. A maimakon haka, yana da matukar jayayya da gardama game da kalmomi. Wadannan kalmomi na kawo kishi, da husuma, da zage-zage, da miyagun zace-zace, da
5 constant friction of people of corrupt minds and destitute of the truth, who suppose that godliness is a means of gain.
yawan rashin jituwa tsakanin mutane masu rubabbun hankula. Sun bijire wa gaskiya. Suna tunani cewa ibada hanya ce ta yin arziki.” Ka zame daga wadannan abubuwa.
6 But godliness with contentment is great gain.
Yanzu bin Allah tare da dangana babbar riba ce.
7 For we brought nothing into the world, so neither can we carry anything out.
Gama ba mu kawo komai a duniya ba, ba zamu iya fita cikinta da komai ba.
8 But having food and clothing, we will be content with that.
A maimakon haka, mu dangana da abinci da kuma sutura.
9 But those who are determined to be rich fall into a temptation and a snare and many foolish and harmful lusts, such as plunge people into ruin and destruction.
To wadanda ke son zama mawadata su kan fada cikin jaraba, cikin tarko. Suna fadawa cikin abubuwan wauta da sha'awoyi masu illa da kowanne abu da ke sa mutane su dulmaya cikin lallacewa da hallaka.
10 For the love of money is a root of all kinds of evil. Some have been led astray from the faith in their greed, and have pierced themselves through with many sorrows.
Gama son kudi shine tushen kowacce irin mugunta. Wadansu mutane garin neman kudi sun kauce daga bangaskiya, sun kuma jawowa kansu bakin ciki mai yawa.
11 But you, man of God, flee these things, and follow after righteousness, godliness, faith, love, patience, and gentleness.
Amma kai, mutumin Allah, ka guji wadannan abubuwa, ka bi adalci, ibada, aminci, kauna, jimiri, da tawali'u.
12 Fight the good fight of faith. Lay hold of the everlasting life to which you were called, and you confessed the good confession in the sight of many witnesses. (aiōnios g166)
Ka yi fama, fama mai kyau na bangaskiya. Ka kama rai madawami da aka kira ka gare shi. A kan wannan ne ka ba da shaida a gaban shaidu masu yawa game da abin da ke da kyau. (aiōnios g166)
13 I command you before God, who gives life to all things, and before Meshikha Yeshua, who before Pontius Pilate testified the good confession,
Ina ba ka wannan umarni a gaban Allah wanda ke rayar da dukan abubuwa, da gaban Almasihu Yesu, wanda ya fadi abin da ke gaskiya ga Bilatus Babunti.
14 that you keep the commandment without spot, blameless, until the appearing of our Lord Yeshua Meshikha;
Ka bi doka daidai, babu abin zargi har bayanuwar Ubangijinmu Yesu Almasihu.
15 which in its own times he will show, who is the blessed and only Ruler, the King of kings, and Lord of lords;
Allah zai nuna bayyanuwarsa a daidai lokaci- Allah, mai albarka, Makadaicin iko, Sarkin da ke sarauta, Ubangiji mai mulki.
16 who alone has immortality, dwelling in unapproachable light; whom no human has seen, nor can see: to whom be honor and eternal power. Amen. (aiōnios g166)
Shine kadai marar mutuwa, mai zama cikin hasken da ba ya kusantuwa. Ba wanda ke ganinsa, ko ya iya hango shi. Girma ya tabbata a gare shi da kuma madawwamin iko. Amin. (aiōnios g166)
17 Charge those who are rich in this present world that they not be haughty, nor have their hope set on the uncertainty of riches, but on God, who richly provides us with everything to enjoy; (aiōn g165)
Ka gaya wa masu dukiya a cikin wannan duniya kada su daga kai, kada su sa bege ga arziki mara dawwama. Maimamakon haka, su sa begensu ga Allah wanda ke ba mu wadatar gaske domin jin dadin mu. (aiōn g165)
18 that they do good, that they be rich in good works, that they be ready to distribute, willing to communicate;
Gaya masu su yi nagarta su arzurta a ayyuka nagari, su zama masu bayarwa hannu sake.
19 laying up in store for themselves a good foundation against the time to come, that they may lay hold of that which is truly life.
Ta haka za su ajiye wa kansu harsashi mai kyau kan abin da ke zuwa domin su amshi rayuwa ta kwarai.
20 Timothy, guard that which is committed to you, turning away from the empty chatter and oppositions of the knowledge which is falsely so called;
Timoti, ka kare abin da aka ba ka. Ka nisanci maganar wauta da gardamomin da ke sabawa juna wanda ake kira ilimi a karyace.
21 which some professing have erred concerning the faith. Grace be with you.
Wadansu mutane suna shelar wadannan abubuwa, don haka sun kauce wa bangaskiyar. Bari alheri ya kasance tare da kai.

< 1 Timothy 6 >