< Psalms 95 >

1 The praise of a Song by David. Come, let us exult in the Lord; let us make a joyful noise to God our Saviour.
Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
2 Let us come before his presence with thanksgiving, and make a joyful noise to him with psalms.
Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
3 For the Lord is a great God, and a great king over all gods: for the Lord will not cast off his people.
Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
4 For the ends of the earth are in his hands; and the heights of the mountains are his.
A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
5 For the sea is his, and he made it: and is hands formed the dry land.
Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
6 Come, let us worship and fall down before him; and weep before the Lord that made us.
Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
7 For he is our God; and we are the people of his pasture, and the sheep of his hand.
gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
8 To-day, if you will hear his voice, harden not your hearts, as in the provocation, according to the day of irritation in the wilderness:
“Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
9 where your fathers tempted me, proved me, and saw my works.
inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
10 Forty years was I grieved with this generation, and said, They do always err in their heart, and they have not known my ways.
Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
11 So I sware in my wrath, They shall not enter into my rest.
Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”

< Psalms 95 >