< Proverbs 1 >

1 The Proverbs of Solomon son of David, who reigned in Israel;
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 to know wisdom and instruction, and to perceive words of understanding;
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 to receive also hard saying, and to understand true justice, and [how] to direct judgment;
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 that he might give subtlety to the simple, and to the young man discernment and understanding.
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 For by the hearing of these a wise man will be wiser, and man of understanding will gain direction;
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 and will understand a parable, and a dark speech; the saying of the wise also, and riddles.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 The fear of the Lord is the beginning of wisdom; and [there is] good understanding to all that practise it: and piety toward God is the beginning of discernment; but the ungodly will set at nothing wisdom and instruction.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Hear, [my] son, the instruction of your father, and reject not the rules of your mother.
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 For you shall receive for your head a crown of graces, and a chain of gold round your neck.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 [My] son, let not ungodly men lead you astray, neither consent you [to them].
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 If they should exhort you, saying, Come with us, partake in blood, and let us unjustly hide the just man in the earth:
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 and let us swallow him alive, as Hades [would], and remove the memorial of him from the earth: (Sheol h7585)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
13 let us seize on his valuable property, and let us fill our houses with spoils:
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 but do you cast in your lot with us, and let us all provide a common purse, and let us have one pouch:
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 go not in the way with them, but turn aside your foot from their paths:
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 [For their feet run to do evil, and are swift to shed blood. ]
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 for nets are not without cause spread for birds.
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 For they that are concerned in murder store up evils for themselves; and the overthrow of transgressors is evil.
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 These are the ways of all that perform lawless deeds; for by ungodliness they destroy their own life.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 Wisdom sings aloud in passages, and in the broad places speaks boldly.
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 And she makes proclamation on the top of the walls, and sits by the gates of princes; and at the gates of the city boldly says,
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 So long as the simple cleave to justice, they shall not be ashamed: but the foolish being lovers of haughtiness, having become ungodly have hated knowledge, and are become subject to reproofs.
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 Behold, I will bring forth to you the utterance of my breath, and I will instruct you in my speech.
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 Since I called, and you did not listen; and I spoke at length, and you gave no heed;
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 but you set at nothing my counsels, and disregarded my reproofs;
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 therefore I also will laugh at your destruction; and I will rejoice against [you] when ruin comes upon you:
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 yes when dismay suddenly comes upon you, and [your] overthrow shall arrive like a tempest; and when tribulation and distress shall come upon you, or when ruin shall come upon you.
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 For it shall be that when you call upon me, I will not listen to you: wicked men shall seek me, but shall not find [me].
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 For they hated wisdom, and did not choose the word of the Lord:
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 neither would they attend to my counsels, but derided my reproofs.
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 Therefore shall they eat the fruits of their own way, and shall be filled with their own ungodliness.
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 For because they wronged the simple, they shall be slain; and an inquisition shall ruin the ungodly.
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 But he that hearkens to me shall dwell in confidence, and shall rest securely from all evil.
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< Proverbs 1 >