< Psalms 69 >

1 For the end, [a Psalm] of David, for alternate [strains]. Save me, O God; for the waters have come in to my soul.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 I am stuck fast in deep mire, and there is no standing: I am come in to the depths of the sea, and a storm has overwhelmed me.
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 I am weary [of] crying, my throat has become hoarse; mine eyes have failed by my waiting on my God.
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 They that hate me without a cause are more than the hairs of my head: my enemies that persecute me unrighteously are strengthened: then I restored that which I took not away.
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 O God, you know my foolishness; and my transgressions are not hidden from you.
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 Let not them that wait on you, O Lord of hosts, be ashamed on my account: let not them that seek you, be ashamed on my account, O God of Israel.
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 For I have suffered reproach for your sake; shame has covered my face.
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 I became strange to my brethren, and a stranger to my mother's children.
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 For the zeal of your house has eaten me up; and the reproaches of them that reproached you are fallen upon me.
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
10 And I bowed down my soul with fasting, and that was made my reproach.
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 And I put on sackcloth for my covering; and I became a proverb to them.
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 They that sit in the gate talked against me, and they that drank wine sang against me.
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 But I [will cry] to you, O Lord, in my prayer; O God, it is a propitious time: in the multitude of your mercy hear me, in the truth of your salvation.
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 Save me from the mire, that I stick not [in it]: let me be delivered from them that hate me, and from the deep waters.
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 Let not the waterflood drown me, nor let the deep swallow me up; neither let the well shut its mouth upon me.
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 Hear me, O Lord; for your mercy is good: according to the multitude of your compassions look upon me.
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 And turn not away your face from your servant; for I am afflicted: hear me speedily.
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 Draw near to my soul and redeem it: deliver me because of mine enemies.
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 For you know my reproach, and my shame, and my confusion; all that afflict me are before you.
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 My soul has waited for reproach and misery; and I waited for one to grieve with me, but there was none; and for one to comfort me, but I found none.
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 They gave [me] also gall for my food, and made me drink vinegar for my thirst.
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 Let their table before them be for a snare, and for a recompense, and for a stumbling block.
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 Let their eyes be darkened that they should not see; and bow down their back continually.
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 Pour out your wrath upon them, and let the fury of your anger take hold on them.
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 Let their habitation be made desolate; and let there be no inhabitant in their tents:
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 Because they persecuted him whom you have struck; and they have added to the grief of my wounds.
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 Add iniquity to their iniquity; and let them not come into your righteousness.
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 Let them be blotted out of the book of the living, and let them not be written with the righteous.
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 I am poor and sorrowful; but the salvation of your countenance has helped me.
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 I will praise the name of my God with a song, I will magnify him with praise;
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
31 and [this] shall please God more than a young calf having horns and hoofs.
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 Let the poor see and rejoice; seek the Lord diligently, and you shall live.
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 For the Lord hears the poor, and does not set at nothing his fettered ones.
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 Let the heavens and the earth raise him, the sea, and all things moving in them.
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 For God will save Sion, and the cities of Judea shall be built; and [men] shall dwell there, and inherit it.
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 And the seed of his servants shall possess it, and they that love his name shall dwell therein.
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.

< Psalms 69 >