< Psalms 62 >

1 For the end, a Psalm of David for Idithun. Shall not my soul be subjected to God? for of him is my salvation.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
2 For he is my God, and my savior; my helper, I shall not be moved very much.
Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
3 How long will you assault a man? you are all slaughtering as with a bowed wall and a broken hedge.
Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
4 They only took counsel to set at nothing mine honor: I ran in thirst: with their mouth they blessed, but with their heart they cursed. (Pause)
Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
5 Nevertheless do you, my soul, be subjected to God; for of him [is] my patient hope.
Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
6 For he [is] my God and my Saviour; my helper, I shall not be moved.
Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
7 In God [is] my salvation and my glory: [he is] the God of my help, and my hope is in God.
Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
8 Hope in him, all you congregation of the people; pour out your hearts before him, for God is our helper. (Pause)
Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
9 But the sons of men are vain; the sons of men are false, so as to be deceitful in the balances; they are all alike [formed] out of vanity.
Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
10 Trust not in unrighteousness, and lust not after robberies: if wealth should flow in, set not your heart upon it.
Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
11 God has spoken once, [and] I have heard these two things, that power is of God;
Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
12 and mercy is your, O Lord; for you will recompense every one according to his works.
kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”

< Psalms 62 >