< Psalms 56 >

1 For the end, concerning the people that were removed from the sanctuary, by David for a memorial, when the Philistines caught him in Geth. Have mercy upon me, O God; for man has trodden me down; all the day long he warring has afflicted me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da murya “Kurciya a Itatuwan Oak Mai Nisa.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Filistiyawa suka kama shi a birnin Gat. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, gama mutane sun tasar mini da zafi; dukan yini suna matsa harinsu.
2 Mine enemies have trodden me down all the day from the dawning of the day; for there are many warring against me.
Masu ɓata sunana suna bina dukan yini; da yawa suna kai mini hari cikin fariyarsu.
3 They shall be afraid, but I will trust in you.
Sa’ad da nake tsoro, zan dogara gare ka.
4 In God I will praise my words; all the day have I hoped in God; I will not fear what flesh shall do to me.
Ga Allah wanda maganarsa nake yabo ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum mai mutuwa zai yi mini?
5 All the day long they have abominated my words; all their devices [are] against me for evil.
Dukan yini sun yi ta juya maganata; kullum suna ƙulle-ƙulle su cuce ni.
6 They will dwell near and hide [themselves]; they will watch my steps, accordingly as I have waited patiently in my soul.
Sun haɗa baki, sun ɓoye, suna kallon takawata suna a shirye su ɗauki raina.
7 You will on no account save them; you will bring down the people in wrath.
Sam, kada ka bari su kuɓuce; cikin fushinka, ya Allah, ka saukar da al’ummai.
8 O God, I have declared my life to you; you has set my tears before you, even according to your promise.
Ka lissafta makokina; ka jera hawayena a littafinka, ba a rubuce suke a cikin littafinka ba?
9 Mine enemies shall be turned back, in the day wherein I shall call upon you; behold, I know that you are my God.
Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.
10 In God, will I praise [his] word; in the Lord will I praise [his] saying.
Ga Allah, wanda nake yabon maganarsa, ga Ubangiji, wanda nake yabon maganarsa,
11 I have hoped in God; I will not be afraid of what man shall do to me.
ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?
12 The vows of your praise, O God, which I will pay, are upon me.
Ina ƙarƙashin alkawari gare ka, ya Allah; zan miƙa hadayuna na godiya gare ka.
13 For you have delivered my soul from death, and my feet from sliding, that I should be well-pleasing before God in the land of the living.
Gama ka cece ni daga mutuwa da kuma ƙafafun daga tuntuɓe, don in yi tafiya a gaban Allah cikin hasken rai.

< Psalms 56 >