< Psalms 17 >

1 A prayer of David. Listen, O Lord of my righteousness, attend to my petition; give ear to my prayer not [uttered] with deceitful lips.
Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
2 Let my judgment come forth from your presence; let mine eyes behold righteousness.
Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
3 You has proved mine heart; you have visited [me] by night; you have tried me as with fire, and unrighteousness has not been found in me: [I am purposed] that my mouth shall not speak [amiss].
Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
4 As for the works of men, by the words of your lips I have guarded [myself from] hard ways.
Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
5 Direct my steps in your paths, that my steps slip not.
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
6 I have cried, for you heard me, O God: incline your ear to me, and listen to my words.
Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 Show the marvels of your mercies, you that save them that hope in you.
Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
8 Keep me as the apple of the eye from those that resist your right hand: you shall screen me by the covering of your wings,
Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 from the face of the ungodly that have afflicted me: mine enemies have compassed about my soul.
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10 They have enclosed [themselves with] their own fat: their mouth has spoken pride.
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11 They have now cast me out and compassed me round about: they have set their eyes [so as] to bow them down to the ground.
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12 They laid wait for me as a lion ready for prey, and like a lion's whelp dwelling in secret [places].
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13 Arise, O Lord, prevent them, and cast them down: deliver my soul from the ungodly: [draw] your sword,
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14 because of the enemies of your hand: O Lord, destroy them from the earth; scatter them in their life, though their belly has been filled with your hidden [treasures]: they have been satisfied with uncleanness, and have left the remnant [of their possessions] to their babes.
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
15 But I shall appear in righteousness before your face: I shall be satisfied when your glory appears.
Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.

< Psalms 17 >