< Psalms 10 >

1 Why stand you afar off, O Lord? [why] do you overlook [us] in times of need, in affliction?
Don me, ya Ubangiji, kake tsaya can da nesa? Me ya sa kake ɓoye kanka a lokutan wahala?
2 While the ungodly one acts proudly, the poor is hotly pursued: [the wicked] are taken in the crafty counsels which they imagine.
Cikin fariyarsa mugun mutum yakan cuci marasa ƙarfi, waɗanda yake kama cikin makircin da ya shirya.
3 Because the sinner praises himself for the desires of his heart; and the unjust one blesses himself.
Yakan yi taƙama da ƙulle-ƙullen zuciyarsa; yana albarkaci mai haɗama yana kuma ƙin Ubangiji.
4 The sinner has provoked the Lord: according to the abundance of his pride he will not seek after [him]: God is not before him.
Cikin ɗaga kai mutum ba ya neman Allah; cikin tunaninsa ba ya ba da wata dama saboda Allah.
5 His ways are profane at all times; your judgments are removed from before him: he will gain the mastery over all his enemies.
Hanyoyinsa kullum sukan yi nasara; yana da girman kai kuma dokokinka suna nesa da shi; yakan yi wa dukan abokan gābansa duban reni.
6 For he has said in his heart, I shall not be moved, [continuing] without evil from generation to generation.
Yakan ce wa kansa, “Ba abin da zai girgiza ni; kullum zan yi murna ba zan taɓa shiga wahala ba.”
7 Whose mouth is full of cursing, and bitterness, and fraud: under his tongue are trouble and pain.
Bakinsa ya cika da zage-zage da ƙarairayi da kuma barazana; wahala da mugunta suna a ƙarƙashin harshensa.
8 He lies in wait with rich [men] in secret places, in order to kill the innocent: his eyes are set against the poor.
Yakan yi kwanto kusa da ƙauyuka; daga kwanton yakan kashe marar laifi. Yana kallon waɗanda za su shiga hannunsa a ɓoye.
9 He lies in wait in secret as a lion in his den: he lies in wait to ravish the poor, to ravish the poor when he draws him [after him]: he will bring him down in his snare.
Yakan yi kwanto a ɓoye kamar zaki. Yakan yi kwanto don yă kama marasa ƙarfi; yakan kama marasa ƙarfi yă ja su cikin ragarsa.
10 He will bow down and fall when he has mastered the poor.
Yakan ragargaza waɗanda suka shiga hannu, su fāɗi; sukan fāɗi a ƙarƙashin ƙarfinsa.
11 For he has said in his heart, God has forgotten: he has turned away his face so as never to look.
Yakan ce wa kansa, “Ai, Allah ya manta; ya rufe fuskarsa ba ya gani.”
12 Arise, O Lord God; let your hand be lifted up: forget not the poor.
Ka tashi, Ubangiji! Ka hukunta miyagu, ya Allah. Kada ka manta da marasa ƙarfi.
13 Therefore, has the wicked provoked God? for he has said in his heart, He will not require [it].
Don me mugun mutum zai ƙi Allah? Don me yakan ce wa kansa, “Allah ba zai nemi hakki daga gare ni ba”?
14 You see [it]; for you do observe trouble and wrath, to deliver them into your hands: the poor has been left to you; you were a helper to the orphan.
Amma kai, ya Allah, kana gani wahala da baƙin ciki; kana lura da yadda suke ɗaukansu a hannu. Marar taimako kan danƙa kansa gare ka; kai ne mai taimakon marayu
15 Break you the arm of the sinner and wicked man: his sin shall be sought for, and shall not be found.
Ka karye hannun mugaye da kuma mugun mutum; ka nemi hakki daga gare shi saboda muguntar da ba za a gane ba.
16 The Lord shall reign for ever, even for ever and ever: you Gentiles shall perish out his land.
Ubangiji Sarkin har abada abadin ne; al’ummai za su hallaka daga ƙasarsa.
17 The Lord has heard the desire of the poor: your ear has inclined to the preparation of their heart;
Kakan ji, ya Ubangiji sha’awar mai shan wahala; kakan ƙarfafa su, ka kuma saurari kukansu,
18 to plead for the orphan and afflicted, that man may no more boast upon the earth.
kana kāre marayu da waɗanda aka danne, domin mutum, wanda yake na duniya kada ƙara haddasa wata razana.

< Psalms 10 >