< Zechariah 9 >

1 The burden of the worde of the Lord in the land of Hadrach: and Damascus shalbe his rest: when the eyes of man, euen of all the tribes of Israel shalbe toward the Lord.
Annabci. Maganar Ubangiji tana gāba da ƙasar Hadrak za tă kuma sauko a kan Damaskus, gama idanun dukan mutane da na kabilan Isra’ila suna a kan Ubangiji,
2 And Hamath also shall border thereby: Tyrus also and Zidon, though they be very wise.
da kuma a kan Hamat ita ma, wadda ta yi iyaka da ita, da kuma a kan Taya da Sidon, ko da yake suna da hikima ƙwarai.
3 For Tyrus did build her selfe a strong holde, and heaped vp siluer as the dust, and golde as the myre of the streetes.
Taya ta gina wa kanta mafaka mai ƙarfi; ta tara azurfa kamar ƙasa, zinariya kuma kamar tarin shara a tituna.
4 Beholde, the Lord wil spoyle her, and he wil smite her power in the Sea, and she shalbe deuoured with fire.
Amma Ubangiji zai karɓe mallakarta, zai hallaka ikonta da take da shi a kan teku, wuta kuma za tă cinye ta.
5 Ashkelon shall see it, and feare, and Azzah also shalbe very sorowfull, and Ekron: for her countenance shalbe ashamed, and the King shall perish from Azzah, and Ashkelon shall not be inhabited.
Ashkelon za tă ga haka ta ji tsoro; Gaza za tă yi birgima cikin azaba, haka Ekron ma, gama za tă fid da zuciya. Gaza za tă rasa sarkinta za a kuma gudu a bar Ashkelon.
6 And the stranger shall dwell in Ashdod, and I wil cut off the pride of the Philistims.
Baƙi za su mallaki Ashdod, kuma zan kawar da girman kan Filistiyawa.
7 And I wil take away his blood out of his mouth, and his abominations from betweene his teeth: but he that remaineth, euen he shalbe for our God, and he shalbe as a prince in Iudah, but Ekron shalbe as a Iebusite.
Zan kawar da jini daga bakinsu, zan kuma cire abincin da aka haramta daga tsakanin haƙoransu. Waɗanda za a bari za su zama na Allahnmu, su kuma zama shugabanni a Yahuda, Ekron kuma za tă zama kamar Yebusiyawa.
8 And I will campe about mine House against the armie, against him that passeth by, and against him that returneth, and no oppressour shall come vpon them any more: for now haue I seene with mine eyes.
Amma zan kāre gidana daga sojoji masu kai da kawowa. Azzalumi ba zai ƙara cin mutanena da yaƙi ba, gama yanzu ina tsaro.
9 Reioyce greatly, O daughter Zion: shoute for ioy, O daughter Ierusalem: beholde, thy King commeth vnto thee: he is iust and saued himselfe, poore and riding vpon an asse, and vpon a colt the foale of an asse.
Ki yi murna ƙwarai, ya Diyar Urushalima! Ki yi sowa, Diyar Urushalima! Duba, ga sarkinki yana zuwa wurinki, mai adalci yana kuma da ceto, mai tawali’u yana kuma hawan jaki, yana a kan ɗan aholaki, a kan’yar jaka.
10 And I wil cut off the charets from Ephraim, and the horse from Ierusalem: the bowe of the battel shalbe broken, and he shall speake peace vnto the heathen, and his dominion shalbe from sea vnto sea, and from the Riuer to the end of the land.
Zan ƙwace kekunan yaƙi daga Efraim, da kuma dawakan yaƙi daga Urushalima, za a kuma karya bakan yaƙi. Zai yi shelar salama ga al’ummai. Mulkinsa zai yaɗu daga teku zuwa teku, daga Kogi kuma zuwa ƙarshen duniya.
11 Thou also shalt be saued through the blood of thy couenant. I haue loosed thy prisoners out of the pit wherein is no water.
Ke kuma, saboda jinin alkawarina da ke, zan’yantar da’yan kurkukunki daga rami marar ruwa.
12 Turne you to the strong holde, ye prisoners of hope: euen to day doe I declare, that I will render the double vnto thee.
Ku koma maɓuya, ya ku’yan kurkuku masu sa zuciya; ko yanzu ma na sanar cewa zan mayar muku ninki biyu.
13 For Iudah haue I bent as a bowe for me: Ephraims hand haue I filled, and I haue raised vp thy sonnes, O Zion, against thy sonnes, O Grecia, and haue made thee as a gyants sword.
Zan lanƙwasa Yahuda yadda nake lanƙwasa bakana, in kuma cika ta da Efraim kamar kibiya. Zan tā da’ya’yanki maza, ya Sihiyona, gāba da’ya’yanki, ya Girka, in kuma mai da ke kamar takobin jarumin yaƙi.
14 And the Lord shalbe seene ouer them, and his arrowe shall go forth as the lightning: and the Lord God shall blowe the trumpet, and shall come forth with the whirlewindes of the South.
Sa’an nan Ubangiji zai bayyana a bisansu; kibiyarsa za tă wulga kamar walƙiya. Ubangiji Mai Iko Duka zai busa ƙaho; zai taho ta cikin guguwa daga kudu,
15 The Lord of hostes shall defend them, and they shall deuoure them, and subdue them with sling stones, and they shall drinke, and make a noyse as thorowe wine, and they shalbe filled like bowles, and as the hornes of the altar.
Ubangiji Maɗaukaki kuma zai tsare su. Za su hallakar su kuma yi nasara da duwatsun majajjawa. Za su sha su yi kururuwa kamar sun sha ruwan inabi; za su cika kamar kwanon da ake amfani don a yayyafa jini a kusurwoyin bagade.
16 And the Lord their God shall deliuer them in that day as the flocke of his people: for they shall be as the stones of the crowne lifted up upon his land.
Ubangiji Allahnsu zai cece su a wannan rana gama su mutanensa ne da kuma garkensa. Za su haska a cikin ƙasarsa kamar lu’ulu’u a rawani.
17 For howe great is his goodnesse! and howe great is his beautie! corne shall make the yong men cherefull, and newe wine the maides.
Za su yi kyan gani da kuma bansha’awa! Hatsi zai sa samari su yi murna, sabon ruwan inabi kuma zai sa’yan mata su yi farin ciki.

< Zechariah 9 >