< Zechariah 6 >

1 Againe, I turned and lift vp mine eyes, and looked: and beholde, there came foure charets out from betweene two mountaines, and the mountaines were mountaines of brasse.
Na sāke ɗaga kai sama, sai ga kekunan yaƙi guda huɗu a gabana suna fitowa tsakanin duwatsu guda biyu, duwatsun tagulla!
2 In the first charet were red horses, and in the second charet blacke horses,
Karusa ta farko tana da jajjayen dawakai, ta biyu kuma baƙaƙen dawakai,
3 And in the thirde charet white horses, and in the fourth charet, horses of diuers colours, and reddish.
ta ukun farare dawakai, ta huɗu kuma dawakai masu ɗigo-ɗigo a dukan jikinsu, dukansu kuwa ƙarfafa.
4 Then I answered, and saide vnto the Angell that talked with mee, What are these, my Lord?
Sai na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
5 And the Angell answered, and sayde vnto mee, These are the foure spirites of the heauen, which goe foorth from standing with the Lord of all the earth.
Mala’ikan ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ruhohi huɗu na sama, waɗanda suka fito daga wurin Ubangiji na dukan duniya.
6 That with the blacke horse went forth into the land of the North, and the white went out after them, and they of diuers colours went forth toward the South countrey.
Wannan mai baƙaƙen dawakai zai nufi wajen ƙasar arewa, mai fararen dawakai zai nufi wajen yamma, sai kuma mai dawakai masu ɗigo-ɗigo a jiki zai nufi wajen kudu.”
7 And the reddish went out, and required to go, and passe through the world, and he sayde, Goe passe through the worlde. So they went thorowout the world.
Da ƙarfafa dawakan suka fito, sai suka yi marmari su ratsa dukan duniya. Sai ya ce, “Ku ratsa dukan duniya!” Saboda haka suka ratsa dukan duniya.
8 Then cryed hee vpon me, and spake vnto me, saying, Beholde, these that goe towarde the North countrey, haue pacified my spirit in the North countrey.
Sai ya kira ni ya ce, “Duba, waɗanda suka nufi wajen ƙasar arewa sun ba wa Ruhuna hutu a ƙasar arewa.”
9 And the worde of the Lord came vnto me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini, ta ce,
10 Take of them of ye captiuitie, euen of Heldai, and of Tobijah, and Iedaiah, which are come from Babel, and come thou the same day, and goe vnto the house of Ioshiah, the sonne of Zephaniah.
“Ka karɓi azurfa da zinariya daga masu zaman bauta Heldai, Tobiya, Yedahiya, waɗanda suka iso daga Babilon. A ranar kuma ka je gidan Yosiya ɗan Zefaniya.
11 Take euen siluer, and golde, and make crownes, and set them vpon the head of Iehoshua, the sonne of Iehozadak the hie Priest,
Ka ɗauki azurfar da zinariyar ka yi rawani, ka ɗora shi a kan babban firist, Yoshuwa ɗan Yehozadak.
12 And speake vnto him, saying, Thus speaketh the Lord of hostes, and sayth, Behold the man whose name is the Branch, and he shall growe vp out of his place, and he shall build the Temple of the Lord.
Ka ce masa ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ga mutumin da sunansa ne Reshe, zai kuma ratse daga inda yake yă gina haikalin Ubangiji.
13 Euen hee shall build the Temple of the Lord, and he shall beare the glory, and shall sit and rule vpon his throne, and he shalbe a Priest vpon his throne, and the counsell of peace shall be betweene them both.
Shi ne zai gina haikalin Ubangiji, za a kuma martaba shi da daraja, zai kuma zauna yă yi mulki a kan kursiyinsa. Zai zama firist a kan kursiyinsa. Kuma a tsakanin biyun za a sami zaman lafiya.’
14 And the crownes shall be to Helem, and to Tobijah, and to Iedaiah, and to Hen the sonne of Zephaniah, for a memoriall in the Temple of the Lord.
Za a ba Heldai, Tobiya, Yedahiya da kuma Hen ɗan Zefaniya kamar abin tunawa a cikin haikalin Ubangiji.
15 And they that are farre off, shall come and build in the Temple of the Lord, and ye shall know, that the Lord of hostes hath sent me vnto you. And this shall come to passe, if ye will obey the voyce of the Lord your God.
Waɗanda suke nesa za su zo su taimaka gina haikalin Ubangiji, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku. Wannan zai faru in kuka yi biyayya sosai ga Ubangiji Allahnku.”

< Zechariah 6 >