< Zechariah 11 >

1 Open thy doores, O Lebanon, and the fire shall deuoure thy cedars.
Buɗe ƙofofinki, ya Lebanon, don wuta ta cinye itatuwan al’ul naki.
2 Houle, firre trees: for the cedar is fallen, because all the mightie are destroyed: houle ye, O okes of Bashan, for ye defesed forest is cut downe.
Yi kuka, ya itacen fir, gama itacen al’ul ya fāɗi; itatuwa masu daraja sun lalace! Ku yi kuka, ku itatuwan oak na Bashan; an sassare itatuwan babban kurmi!
3 There is the voyce of the houling of the shepherdes: for their glorie is destroyed: the voyce of ye roaring of lyons whelpes: for the pride of Iorden is destroyed.
Ku ji kukan makiyaya; an ɓata musu wuraren kiwonsu masu ciyayi! Ku ji rurin zakoki; an lalatar da jejin Urdun!
4 Thus sayeth the Lord my God, Feede the sheepe of the slaughter.
Ga abin da Ubangiji Allahna ya ce, “Yi kiwon garken tumakin da za a yanka.
5 They that possesse them, slay them and sinne not: and they that sell them, say, Blessed be the Lord: for I am riche, and their owne shepherds spare them not.
Masu sayensu sun yanyanka su, suka kuwa tafi ba hukunci. Masu sayar da su sun ce, ‘Yabi Ubangiji, na yi arziki!’ Makiyayansu ma ba su ji tausayinsu ba.
6 Surely I wil no more spare those that dwell in the land, sayth the Lord: but loe, I will deliuer the men euery one into his neighbours hand, and into the hand of his King: and they shall smite the land, and out of their hands I wil not deliuer them.
Gama ba zan ƙara jin tausayin mutanen ƙasar ba,” in ji Ubangiji. “Zan ba da kowa ga maƙwabcinsa da kuma sarkinsa. Za su zalunci ƙasar, ba zan kuma cece su daga hannuwansu ba.”
7 For I fed the sheepe of slaughter, euen the poore of the flocke, and I tooke vnto me two staues: the one I called Beautie, and the other I called Bandes, and I fed the sheepe.
Saboda haka na yi kiwon garken da za a yanka, musamman garken da ake zalunta. Sai na ɗauki sanduna biyu na kira ɗaya Tagomashi, ɗaya kuma Haɗinkai, sai na yi kiwon garken.
8 Three shepherdes also I cut off in one moneth, and my soule lothed them, and their soule abhorred me.
Cikin wata guda na kawar da makiyayan nan uku. Garken suka ƙi ni, na kuwa gaji da su
9 Then said I, I will not feede you: that that dyeth, let it dye: and that that perisheth, let it perish: and let the remnant eate, euery one the flesh of his neighbour.
na ce, “Ba zan zama makiyayinku ba. Bari masu mutuwa su mutu, masu hallaka kuma su hallaka. Bari waɗanda suka ragu su ci naman juna.”
10 And I tooke my staffe, euen Beautie, and brake it, that I might disanull my couenant, which I had made with all people.
Sai na ɗauki sandana mai suna Tagomashi na karya shi, na janye alkawarin da na yi da dukan al’ummai.
11 And it was broken in that day: and so the poore of the sheepe that waited vpon me, knew that it was the worde of the Lord.
An janye shi a ranan nan, saboda haka garken da yake cikin wahala masu kallona sun san cewa maganar Ubangiji ce.
12 And I said vnto them, If ye thinke it good, giue me my wages: and if no, leaue off: so they weighed for my wages thirtie pieces of siluer.
Na faɗa musu cewa, “In kun ga ya fi kyau, ku biya ni; in kuwa ba haka ba, ku riƙe.” Saboda haka suka biya ni azurfa talatin.
13 And the Lord said vnto me, Cast it vnto the potter: a goodly price, that I was valued at of them. And I tooke the thirtie pieces of siluer, and cast them to the potter in the house of the Lord.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Jefar da shi cikin ma’aji,” Lada mai kyau da aka yi cinikina ne! Saboda haka sai na ɗauki azurfa talatin ɗin na jefa su cikin gidan Ubangiji don a sa cikin ma’aji.
14 Then brake I mine other staffe, euen the Bandes, that I might dissolue the brotherhood betweene Iudah and Israel.
Sai na karya sandana na biyu mai suna Haɗinkai, ta haka na karya’yan’uwantakar da take tsakanin Yahuda da Isra’ila.
15 And the Lord said vnto me, Take to thee yet the instruments of a foolish shepheard.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka sāke ɗaukar kayan aiki na wawan makiyayi.
16 For loe, I will rayse vp a shepheard in the land, which shall not looke for the thing, that is lost, nor seeke the tender lambes, nor heale that that is hurt, nor feede that that standeth vp: but he shall eate the flesh of the fat, and teare their clawes in pieces.
Gama zan tā da makiyayi a ƙasar wanda ba zai kula da ɓatattu, ko yă nemi ƙanana, ko yă warkar da waɗanda suka ji ciwo, ko kuma ciyar da masu lafiya ba, sai dai zai ci naman keɓaɓɓun tumaki, yă farfasa kofatonsu.
17 O idole shepheard that leaueth the flocke: the sword shalbe vpon his arme, and vpon his right eye. His arme shall be cleane dryed vp, and his right eye shall be vtterly darkened.
“Kaito ga banzan makiyayin nan, wanda ya bar garken! Bari takobi yă sare hannunsa da idonsa na dama! Bari hannunsa yă shanye gaba ƙaf, idonsa na dama kuma yă makance sarai!”

< Zechariah 11 >