< Psalms 94 >

1 O Lord God the auenger, O God the auenger, shewe thy selfe clearely.
Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
2 Exalt thy selfe, O Iudge of the worlde, and render a reward to the proude.
Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
3 Lord how long shall the wicked, how long shall the wicked triumph?
Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
4 They prate and speake fiercely: all the workers of iniquitie vaunt themselues.
Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
5 They smite downe thy people, O Lord, and trouble thine heritage.
Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
6 They slay the widowe and the stranger, and murder the fatherlesse.
Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
7 Yet they say, The Lord shall not see: neither will the God of Iaakob regard it.
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
8 Vnderstande ye vnwise among the people: and ye fooles, when will ye be wise?
Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
9 Hee that planted the eare, shall hee not heare? or he that formed the eye, shall he not see?
Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
10 Or he that chastiseth the nations, shall he not correct? hee that teacheth man knowledge, shall he not knowe?
Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
11 The Lord knoweth the thoughtes of man, that they are vanitie.
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
12 Blessed is the man, whom thou chastisest, O Lord, and teachest him in thy Lawe,
Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
13 That thou mayest giue him rest from the dayes of euill, whiles the pitte is digged for the wicked.
kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
14 Surely the Lord will not faile his people, neither will he forsake his inheritance.
Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
15 For iudgement shall returne to iustice, and all the vpright in heart shall follow after it.
Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
16 Who will rise vp with me against the wicked? or who will take my part against the workers of iniquitie?
Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
17 If the Lord had not holpen me, my soule had almost dwelt in silence.
Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
18 When I said, My foote slideth, thy mercy, O Lord, stayed me.
Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
19 In the multitude of my thoughts in mine heart, thy comfortes haue reioyced my soule.
Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
20 Hath the throne of iniquitie fellowship with thee, which forgeth wrong for a Lawe?
Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
21 They gather them together against the soule of the righteous, and condemne the innocent blood.
Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
22 But the Lord is my refuge, and my God is the rocke of mine hope.
Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
23 And hee will recompence them their wickednes, and destroy them in their owne malice: yea, the Lord our God shall destroy them.
Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.

< Psalms 94 >