< Proverbs 1 >

1 The Parables of Salomon the sonne of Dauid King of Israel,
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 To knowe wisdome, and instruction, to vnderstand ye wordes of knowledge,
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 To receiue instruction to do wisely, by iustice and iudgement and equitie,
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 To giue vnto the simple, sharpenesse of wit, and to the childe knowledge and discretion.
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 A wise man shall heare and increase in learning, and a man of vnderstanding shall attayne vnto wise counsels,
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 To vnderstand a parable, and the interpretation, the wordes of ye wise, and their darke sayings.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 The feare of the Lord is the beginning of knowledge: but fooles despise wisedome and instruction.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 My sonne, heare thy fathers instruction, and forsake not thy mothers teaching.
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 For they shalbe a comely ornament vnto thine head, and as chaines for thy necke.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 My sonne, if sinners doe intise thee, consent thou not.
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 If they say, Come with vs, we will lay waite for blood, and lie priuilie for the innocent without a cause:
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 We wil swallow them vp aliue like a graue euen whole, as those that goe downe into the pit: (Sheol h7585)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
13 We shall finde all precious riches, and fill our houses with spoyle:
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 Cast in thy lot among vs: we will all haue one purse:
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 My sonne, walke not thou in the way with them: refraine thy foote from their path.
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 For their feete runne to euill, and make haste to shed blood.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 Certainely as without cause the net is spred before the eyes of all that hath wing:
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 So they lay waite for blood and lie priuily for their liues.
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 Such are the wayes of euery one that is greedy of gaine: he would take away the life of the owners thereof.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 Wisdome cryeth without: she vttereth her voyce in the streetes.
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 She calleth in the hye streete, among the prease in the entrings of the gates, and vttereth her wordes in the citie, saying,
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 O ye foolish, howe long will ye loue foolishnes? and the scornefull take their pleasure in scorning, and the fooles hate knowledge?
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 (Turne you at my correction: loe, I will powre out my mind vnto you, and make you vnderstand my wordes)
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 Because I haue called, and ye refused: I haue stretched out mine hand, and none woulde regarde.
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 But ye haue despised all my counsell, and would none of my correction.
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 I will also laugh at your destruction, and mocke, when your feare commeth.
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 Whe your feare cometh like sudden desolation, and your destruction shall come like a whirle wind: whe affliction and anguish shall come vpon you,
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 Then shall they call vpon me, but I will not answere: they shall seeke me early, but they shall not finde me,
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 Because they hated knowledge, and did not chuse the feare of the Lord.
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 They would none of my counsell, but despised all my correction.
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 Therefore shall they eate of ye fruite of their owne way, and be filled with their owne deuises.
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 For ease slaieth the foolish, and the prosperitie of fooles destroyeth them.
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 But he that obeyeth me, shall dwell safely, and be quiet from feare of euill.
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< Proverbs 1 >