< Psalms 86 >

1 A prayer of David. Incline thine eare, O Lord, and heare me: for I am poore and needy.
Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
2 Preserue thou my soule, for I am mercifull: my God, saue thou thy seruant, that trusteth in thee.
Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
3 Be mercifull vnto me, O Lord: for I crie vpon thee continually.
Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
4 Reioyce the soule of thy seruant: for vnto thee, O Lord, doe I lift vp my soule.
Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
5 For thou, Lord, art good and mercifull, and of great kindenes vnto all them, that call vpon thee.
Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
6 Giue eare, Lord, vnto my prayer, and hearken to the voyce of my supplication.
Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
7 In the day of my trouble I will call vpon thee: for thou hearest me.
A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
8 Among the gods there is none like thee, O Lord, and there is none that can doe like thy workes.
A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
9 All nations, whome thou hast made, shall come and worship before thee, O Lord, and shall glorifie thy Name.
Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
10 For thou art great and doest wonderous things: thou art God alone.
Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
11 Teach me thy way, O Lord, and I will walke in thy trueth: knit mine heart vnto thee, that I may feare thy Name.
Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
12 I wil prayse thee, O Lord my God, with all mine heart: yea, I wil glorifie thy Name for euer.
Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
13 For great is thy mercie toward me, and thou hast deliuered my soule from the lowest graue. (Sheol h7585)
Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol h7585)
14 O God, the proude are risen against me, and the assemblies of violent men haue sought my soule, and haue not set thee before them.
Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
15 But thou, O Lord, art a pitifull God and mercifull, slowe to anger and great in kindenes and trueth.
Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
16 Turne vnto me, and haue mercy vpon me: giue thy strength vnto thy seruant, and saue the sonne of thine handmayd.
Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
17 Shew a token of thy goodnes towarde me, that they which hate me, may see it, and be ashamed, because thou, O Lord, hast holpen me and comforted me.
Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.

< Psalms 86 >