< Psalms 56 >

1 To him that excelleth. A Psalme of David on Michtam, concerning the dumme doue in a farre countrey, when the Philistims tooke him in Gath. Be mercifull vnto me, O God, for man would swallow me vp: he fighteth continually and vexeth me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da murya “Kurciya a Itatuwan Oak Mai Nisa.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Filistiyawa suka kama shi a birnin Gat. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, gama mutane sun tasar mini da zafi; dukan yini suna matsa harinsu.
2 Mine enemies would dayly swallowe mee vp: for many fight against me, O thou most High.
Masu ɓata sunana suna bina dukan yini; da yawa suna kai mini hari cikin fariyarsu.
3 When I was afrayd, I trusted in thee.
Sa’ad da nake tsoro, zan dogara gare ka.
4 I will reioyce in God, because of his word, I trust in God, and will not feare what flesh can doe vnto me.
Ga Allah wanda maganarsa nake yabo ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum mai mutuwa zai yi mini?
5 Mine owne wordes grieue me dayly: all their thoughtes are against me to doe me hurt.
Dukan yini sun yi ta juya maganata; kullum suna ƙulle-ƙulle su cuce ni.
6 They gather together, and keepe them selues close: they marke my steps, because they waite for my soule.
Sun haɗa baki, sun ɓoye, suna kallon takawata suna a shirye su ɗauki raina.
7 They thinke they shall escape by iniquitie: O God, cast these people downe in thine anger.
Sam, kada ka bari su kuɓuce; cikin fushinka, ya Allah, ka saukar da al’ummai.
8 Thou hast counted my wandrings: put my teares into thy bottel: are they not in thy register?
Ka lissafta makokina; ka jera hawayena a littafinka, ba a rubuce suke a cikin littafinka ba?
9 When I cry, then mine enemies shall turne backe: this I know, for God is with me.
Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.
10 I will reioyce in God because of his worde: in the Lord wil I reioyce because of his worde.
Ga Allah, wanda nake yabon maganarsa, ga Ubangiji, wanda nake yabon maganarsa,
11 In God doe I trust: I will not be afrayd what man can doe vnto me.
ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?
12 Thy vowes are vpon me, O God: I will render prayses vnto thee.
Ina ƙarƙashin alkawari gare ka, ya Allah; zan miƙa hadayuna na godiya gare ka.
13 For thou hast deliuered my soule from death, and also my feete from falling, that I may walke before God in the light of the liuing.
Gama ka cece ni daga mutuwa da kuma ƙafafun daga tuntuɓe, don in yi tafiya a gaban Allah cikin hasken rai.

< Psalms 56 >