< Psalms 4 >

1 To him that excelleth on Neginoth. A Psalme of Dauid. Heare me when I call, O God of my righteousnes: thou hast set me at libertie, when I was in distresse: haue mercie vpon me and hearken vnto my prayer.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
2 O ye sonnes of men, howe long will yee turne my glory into shame, louing vanitie, and seeking lyes? (Selah)
Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
3 For be ye sure that the Lord hath chosen to himselfe a godly man: the Lord will heare when I call vnto him.
Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
4 Tremble, and sinne not: examine your owne heart vpon your bed, and be still. (Selah)
Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
5 Offer the sacrifices of righteousnes, and trust in the Lord.
Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
6 Many say, Who will shewe vs any good? but Lord, lift vp the light of thy countenance vpon vs.
Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
7 Thou hast giuen mee more ioye of heart, then they haue had, when their wheate and their wine did abound.
Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
8 I will lay mee downe, and also sleepe in peace: for thou, Lord, onely makest me dwell in safetie.
Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.

< Psalms 4 >