< Psalms 35 >

1 A Psalme of Dauid. Pleade thou my cause, O Lord, with them that striue with me: fight thou against them, that fight against me.
Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
2 Lay hand vpon the shielde and buckler, and stand vp for mine helpe.
Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
3 Bring out also the speare and stop the way against them, that persecute me: say vnto my soule, I am thy saluation.
Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
4 Let them be confounded and put to shame, that seeke after my soule: let them be turned backe, and brought to confusion, that imagine mine hurt.
Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
5 Let them be as chaffe before the winde, and let the Angel of the Lord scatter them.
Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
6 Let their way be darke and slipperie: and let the Angel of the Lord persecute them.
bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
7 For without cause they haue hid the pit and their net for me: without cause haue they digged a pit for my soule.
Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
8 Let destruction come vpon him at vnwares, and let his net, that he hath laid priuilie, take him: let him fall into the same destruction.
bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
9 Then my soule shalbe ioyfull in the Lord: it shall reioyce in his saluation.
Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
10 All my bones shall say, Lord, who is like vnto thee, which deliuerest the poore from him, that is too strong for him! yea, the poore and him that is in miserie, from him that spoyleth him!
Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
11 Cruell witnesses did rise vp: they asked of me things that I knewe not.
Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
12 They rewarded me euill for good, to haue spoyled my soule.
Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
13 Yet I, when they were sicke, I was clothed with a sacke: I humbled my soule with fasting: and my praier was turned vpon my bosome.
Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
14 I behaued my selfe as to my friend, or as to my brother: I humbled my selfe, mourning as one that bewaileth his mother.
nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
15 But in mine aduersitie they reioyced, and gathered them selues together: the abiects assembled themselues against me, and knewe not: they tare me and ceased not,
Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
16 With the false skoffers at bankets, gnashing their teeth against me.
Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
17 Lord, how long wilt thou beholde this? deliuer my soule from their tumult, euen my desolate soule from the lions.
Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
18 So will I giue thee thankes in a great Congregation: I will praise thee among much people.
Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
19 Let not them that are mine enemies, vniustly reioyce ouer mee, neyther let them winke with the eye, that hate mee without a cause.
Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
20 For they speake not as friendes: but they imagine deceitfull woordes against the quiet of the lande.
Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
21 And they gaped on mee with their mouthes, saying, Aha, aha, our eye hath seene.
Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
22 Thou hast seene it, O Lord: keepe not silence: be not farre from me, O Lord.
Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
23 Arise and wake to my iudgement, euen to my cause, my God, and my Lord.
Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
24 Iudge me, O Lord my God, according to thy righteousnesse, and let them not reioyce ouer mee.
Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
25 Let them not say in their hearts, O our soule reioyce: neither let them say, We haue deuoured him.
Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
26 Let them bee confounded, and put to shame together, that reioyce at mine hurt: let them bee clothed with confusion and shame, that lift vp themselues against me.
Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
27 But let them be ioyful and glad, that loue my righteousnesse: yea, let them say alway, Let the Lord be magnified, which loueth the prosperitie of his seruant.
Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
28 And my tongue shall vtter thy righteousnesse, and thy praise euery day.
Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.

< Psalms 35 >