< Psalms 25 >

1 A Psalme of David. Unto thee, O Lord, lift I vp my soule.
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
2 My God, I trust in thee: let me not be confounded: let not mine enemies reioyce ouer mee.
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
3 So all that hope in thee, shall not be ashamed: but let them be confounded, that transgresse without cause.
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
4 Shew me thy waies, O Lord, and teache me thy paths.
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
5 Leade me foorth in thy trueth, and teache me: for thou art the God of my saluation: in thee doe I trust all the day.
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
6 Remember, O Lord, thy tender mercies, and thy louing kindnesse: for they haue beene for euer.
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
7 Remember not the sinnes of my youth, nor my rebellions, but according to thy kindenesse remember thou me, euen for thy goodnesse sake, O Lord.
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
8 Gracious and righteous is the Lord: therefore will he teache sinners in the way.
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
9 Them that be meeke, will hee guide in iudgement, and teach the humble his way.
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
10 All the pathes of the Lord are mercie and trueth vnto such as keepe his couenant and his testimonies.
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
11 For thy Names sake, O Lord, be merciful vnto mine iniquitie, for it is great.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
12 What man is he that feareth the Lord? him wil he teache the way that hee shall chuse.
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
13 His soule shall dwell at ease, and his seede shall inherite the land.
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
14 The secrete of the Lord is reueiled to them, that feare him: and his couenant to giue them vnderstanding.
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
15 Mine eyes are euer towarde the Lord: for he will bring my feete out of the net.
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
16 Turne thy face vnto mee, and haue mercie vpon me: for I am desolate and poore.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17 The sorowes of mine heart are enlarged: drawe me out of my troubles.
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
18 Looke vpon mine affliction and my trauel, and forgiue all my sinnes.
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19 Beholde mine enemies, for they are manie, and they hate me with cruell hatred.
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20 Keepe my soule, and deliuer me: let me not be confounded, for I trust in thee.
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
21 Let mine vprightnes and equitie preserue me: for mine hope is in thee.
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
22 Deliuer Israel, O God, out of all his troubles.
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!

< Psalms 25 >