< Psalms 14 >

1 To him that excelleth. A Psalme of Dauid. The foole hath said in his heart, There is no God: they haue corrupted, and done an abominable worke: there is none that doeth good.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Wawaye sukan ce a ransu, “Ba Allah.” Sun lalace, ayyukansu kuwa mugaye ne; babu wani da yake yi abu mai kyau.
2 The Lord looked downe from heauen vpon the children of men, to see if there were any that would vnderstand, and seeke God.
Ubangiji ya duba daga sama a kan’yan adam don yă ga ko akwai wani da ya gane, wani wanda yake neman Allah.
3 All are gone out of the way: they are all corrupt: there is none that doeth good, no not one.
Duka sun kauce, duka gaba ɗaya sun zama lalatattu; babu ɗaya wanda yake yin abu mai kyau, ba ko ɗaya.
4 Doe not all the workers of iniquitie know that they eate vp my people, as they eate bread? they call not vpon the Lord.
Masu aikata mugunta za su taɓa koyo. Suna cin mutane yadda mutane ke cin gurasa kuma waɗanda ba sa kira bisa Ubangiji?
5 There they shall be taken with feare, because God is in the generation of the iust.
Ga su, tsoro ya sha kansu, gama Allah yana cikin ƙungiyar adalai.
6 You haue made a mocke at the counsell of the poore, because the Lord is his trust.
Ku masu mugunta kuna sa ƙoƙarin matalauta yă zama banza, amma Ubangiji ne mafakansu.
7 Oh giue saluation vnto Israel out of Zion: when the Lord turneth the captiuitie of his people, then Iaakob shall reioyce, and Israel shall be glad.
Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Ubangiji zai maido da sa’ar mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!

< Psalms 14 >