< Psalms 135 >

1 Praise ye the Lord. Praise the Name of the Lord: ye seruants of the Lord, praise him.
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 Ye that stande in the House of the Lord, and in the courtes of the House of our God,
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 Praise ye the Lord: for the Lord is good: sing praises vnto his Name: for it is a comely thing.
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 For the Lord hath chosen Iaakob to himselfe, and Israel for his chiefe treasure.
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 For I know that the Lord is great, and that our Lord is aboue all gods.
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 Whatsoeuer pleased the Lord, that did hee in heauen and in earth, in the sea, and in all the depths.
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 He bringeth vp the cloudes from the ends of the earth, and maketh the lightnings with ye raine: he draweth foorth the winde out of his treasures.
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 He smote the first borne of Egypt both of man and beast.
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 He hath sent tokens and wonders into the middes of thee, O Egypt, vpon Pharaoh, and vpon all his seruants.
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 He smote many nations, and slew mightie Kings:
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 As Sihon King of the Amorites, and Og King of Bashan, and all the kingdomes of Canaan:
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 And gaue their lande for an inheritance, euen an inheritance vnto Israel his people.
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 Thy Name, O Lord, endureth for euer: O Lord, thy remembrance is from generation to generation.
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 For the Lord will iudge his people, and be pacified towardes his seruants.
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 The idoles of the heathen are siluer and golde, euen the worke of mens handes.
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 They haue a mouth, and speake not: they haue eyes and see not.
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 They haue eares and heare not, neither is there any breath in their mouth.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 They that make them, are like vnto them: so are all that trust in them.
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 Praise the Lord, ye house of Israel: praise the Lord, ye house of Aaron.
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 Praise the Lord, ye house of Leui: ye that feare the Lord, praise the Lord.
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 Praised bee the Lord out of Zion, which dwelleth in Ierusalem. Praise ye the Lord.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Psalms 135 >