< Psalms 116 >

1 I love the Lord, because he hath heard my voyce and my prayers.
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
2 For he hath inclined his eare vnto me, whe I did call vpon him in my dayes.
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
3 When the snares of death copassed me, and the griefes of the graue caught me: when I founde trouble and sorowe. (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
4 Then I called vpon the Name of the Lord, saying, I beseech thee, O Lord, deliuer my soule.
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
5 The Lord is mercifull and righteous, and our God is full of compassion.
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
6 The Lord preserueth the simple: I was in miserie and he saued me.
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
7 Returne vnto thy rest, O my soule: for the Lord hath bene beneficiall vnto thee,
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
8 Because thou hast deliuered my soule from death, mine eyes from teares, and my feete from falling.
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
9 I shall walke before the Lord in the lande of the liuing.
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
10 I beleeued, therefore did I speake: for I was sore troubled.
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
11 I said in my feare, All men are lyers.
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
12 What shall I render vnto the Lord for all his benefites toward me?
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
13 I will take the cup of saluation, and call vpon the Name of the Lord.
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
14 I will pay my vowes vnto the Lord, euen nowe in the presence of all his people.
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
15 Precious in the sight of the Lord is the death of his Saintes.
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
16 Beholde, Lord: for I am thy seruant, I am thy seruant, and the sonne of thine handmaide: thou hast broken my bondes.
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
17 I will offer to thee a sacrifice of prayse, and will call vpon the Name of the Lord.
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
18 I will pay my vowes vnto the Lord, euen nowe in the presence of all his people,
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
19 In the courtes of ye Lords house, euen in the middes of thee, O Ierusalem. Praise ye the Lord.
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Psalms 116 >