< Psalms 112 >

1 Praise ye the Lord. Blessed is the man, that feareth the Lord, and deliteth greatly in his commandements.
Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
2 His seede shall be mightie vpon earth: the generation of the righteous shall be blessed.
’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
3 Riches and treasures shalbe in his house, and his righteousnesse endureth for euer.
Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
4 Vnto the righteous ariseth light in darkenes: he is merciful and full of copassion and righteous.
Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
5 A good man is mercifull and lendeth, and will measure his affaires by iudgement.
Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
6 Surely he shall neuer be moued: but the righteous shalbe had in euerlasting remembrance.
Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
7 He will not be afraide of euill tidings: for his heart is fixed, and beleeueth in the Lord.
Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
8 His heart is stablished: therefore he will not feare, vntill he see his desire vpon his enemies.
Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
9 He hath distributed and giuen to ye poore: his righteousnesse remaineth for euer: his horne shalbe exalted with glory.
Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
10 The wicked shall see it and be angrie: he shall gnash with his teeth, and consume away: the desire of the wicked shall perish.
Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.

< Psalms 112 >