< Numbers 26 >

1 And so after the plague, the Lord spake vnto Moses, and to Eleazar the sonne of Aaron the Priest, saying,
Bayan annobar, sai Ubangiji ya yi magana da Musa da Eleyazar ɗan Haruna, firist ya ce,
2 Take the nomber of all the Congregation of the children of Israel from twentie yeere olde and aboue throughout their fathers houses, all that go forth to warre in Israel.
“Ku ƙidaya dukan jama’ar Isra’ila daga mai shekaru ashirin zuwa gaba da za su iya aikin sojan Isra’ila.”
3 So Moses and Eleazar the Priest spake vnto them in the plaine of Moab, by Iorden towarde Iericho, saying,
Musa da Eleyazar firist suka yi musu magana a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko, suka ce,
4 From twentie yeere olde and aboue ye shall nomber the people, as the Lord had commanded Moses, and the childre of Israel, when they came out of the land of Egypt.
“Ku ƙidaya maza daga mai shekara ashirin zuwa gaba yadda Ubangiji ya umarci Musa.” Waɗannan su ne Isra’ilawan da suka fito daga Masar.
5 Reuben the first borne of Israel: the children of Reube were: Hanoch, of whom came the familie of the Hanochites, and of Pallu the familie of the Palluites:
Zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila, daga Hanok; kabilar Hanokawa; daga Fallu; kabilar Falluyawa;
6 Of Hesron, the familie of the Hesronites: of Carmi, the familie of the Carmites.
daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Karmi, kabilar Karmiyawa.
7 These are the families of the Reubenites: and they were in nomber three and fourtie thousand, seuen hundreth and thirtie.
Waɗannan su ne kabilan Ruben; jimillarsu ta kai 43,730.
8 And the sonnes of Pallu, Eliab:
Ɗan Fallu kuwa shi ne Eliyab,
9 And the sonnes of Eliab, Nemuel, and Dathan, and Abiram: this Dathan and Abiram were famous in the Congregation, and stroue against Moses and against Aaron in the assemblie of Korah, when they stroue against the Lord.
’ya’yan Eliyab maza kuwa su ne, Nemuwel, Datan da Abiram. Datan da Abiram nan, su ne shugabannin mutanen da suka tayar wa Musa da Haruna, suna kuma cikin waɗanda suka bi Kora sa’ad da ya tayar wa Ubangiji.
10 And the earth opened her mouth, and swalowed them vp with Korah, when the Congregation died, what time the fire consumed, two hundreth and fiftie men, who were for a signe.
Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora, wanda ƙungiyarsa ta mutu sa’ad da wuta ta cinye mutum 250. Wannan kuwa ya zama alamar faɗakarwa.
11 Notwithstanding, all the sonnes of Korah dyed not.
Amma fa, zuriyar Kora ba tă mutu ba.
12 And the children of Simeon after their families were: Nemuel, of whom came the familie of the Nemuelites: of Iamin, the familie of the Iaminites: of Iachin, the familie of the Iachinites:
Zuriyar Simeyon bisa ga kabilansu, daga Nemuwel, kabilar Nemuwelawa; daga Yamin, kabilar Yaminawa; daga Yakin, kabilar Yakinawa;
13 Of Zerah, the familie of the Zarhites: of Shaul, the familie of the Shaulites.
daga Zera, kabilar Zerawa; daga Sha’ul, kabilar Sha’ul.
14 These are the families of the Simeonites: two and twentie thousand and two hundreth.
Waɗannan su ne kabilan Simeyon; jimillarsu ta kai 22,200.
15 The sonnes of Gad after their families were: Zephon, of whome came ye familie of the Zephonites: of Haggi, the familie of the Haggites: of Shuni, the familie of the Shunites:
Zuriyar Gad bisa ga kabilansu, daga Zafon, kabilar Zafonawa; daga Haggi, kabilar Haggiwa; daga Shuni, kabilar Shunawa;
16 Of Ozni, the familie of the Oznites: of Eri, the familie of the Erites:
daga Ozni, kabilar Ozniyawa daga Eri, kabilar Eriyawa;
17 Of Arod, the familie of the Arodites: of Areli, the familie of the Arelites.
daga Arod, kabilar Arodiyawa; daga Areli, kabilar Areliyawa.
18 These are the families of the sonnes of Gad, according to their nombers, fourtie thousand and fiue hundreth.
Waɗannan su ne kabilan Gad, jimillarsu ta kai 40,500.
19 The sonnes of Iudah, Er and Onan: but Er and Onan died in the land of Canaan.
Er da Onan,’ya’yan Yahuda ne, amma sun mutu a Kan’ana.
20 So were the sonnes of Iudah after their families: of Shelah came the familie of ye Shelanites: of Pharez, the familie of the Pharzites, of Zerah, the familie of the Zarhites.
Zuriyar Yahuda bisa ga kabilansu, daga Shela, kabilar Shelayawa daga Ferez, kabilar Ferezawa; daga Zera, kabilar Zerawa;
21 And the sonnes of Pharez were: of Hesron, the familie of the Hesronites: of Hamul, the familie of the Hamulites.
Zuriyar Ferez kuwa, daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Hamul; kabilar Hamulawa.
22 These are the families of Iudah, after their nombers, seuentie and sixe thousande and fiue hundreth.
Waɗannan su ne kabilan Yahuda; jimillarsu ta kai 76,500.
23 The sonnes of Issachar, after their families were: Tola, of whom came the familie of the Tolaites: of Pua, the familie of the Punites:
Zuriyar Issakar bisa ga kabilansu, daga Tola, kabilar Tolatawa; daga Fuwa, kabilar Fuwayawa;
24 Of Iashub the familie of the Iashubites: of Shimron, the familie of the Shimronites.
daga Yashub, kabilar Yashubawa; daga Shimron, kabilar Shimronawa.
25 These are the families of Issachar, after their nombers, threescore and foure thousand and three hundreth.
Waɗannan su ne kabilan Issakar; jimillarsu ta kai 64,300.
26 The sonnes of Zebulun, after their families were: of Sered, the familie of the Sardites: of Elon, the familie of the Elonites: of Iahleel, the familie of the Iahleelites.
Zuriyar Zebulun bisa ga kabilansu, daga Sered, kabilar Seredawa; daga Elon kabilar Elonawa; daga Yaleyel; kabilar Yaleyewa.
27 These are the families of the Zebulunites, after their nombers, three score thousande and fiue hundreth.
Waɗannan su ne kabilan Zebulun, jimillarsu ta kai 60,500.
28 The sonnes of Ioseph, after their families were Manasseh and Ephraim.
Zuriyar Yusuf bisa ga kabilansu ta wurin Manasse da Efraim.
29 The sonnes of Manasseh were: of Machir, the familie of the Machirites: and Machir begate Gilead: of Gilead came the familie of the Gileadites.
Zuriyar Manasse, daga Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Gileyad); daga Gileyad, kabilar Gileyadawa.
30 These are the sonnes of Gilead: of Iezer, the familie of the Iezerites: of Helek, the familie of the Helekites.
Waɗannan su ne zuriya Gileyad, daga Iyezer, kabilar Iyezerawa; daga Helek, kabilar Helekawa;
31 Of Asriel, the familie of the Asrielites: of Shechem, the familie of Shichmites.
daga Asriyel, kabilar Asriyelawa; daga Shekem, kabilar Shekem;
32 Of Shemida, the familie of the Shemidaites: of Hepher, the familie of the Hepherites.
daga Shemida, kabilar Shemadawa; daga Hefer, kabilar Heferawa.
33 And Zelophehad the sonne of Hepher had no sonnes, but daughters: and the names of the daughters of Zelophehad were Mahlah, and Noah, Hoglah, Milcah and Tirzah.
(Zelofehad ɗan Hefer, ba shi da’ya’ya maza;’yan mata ne kaɗai ya haifa, sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.)
34 These are the families of Manasseh, and the nomber of them, two and fiftie thousand and seuen hundreth.
Waɗannan su ne kabilan Manasse, jimillarsu ta kai 52,700.
35 These are the sonnes of Ephraim after their families: of Shuthelah came the familie of the Shuthalhites: of Becher, the familie of the Bachrites: of Tahan, the familie of the Tahanites.
Waɗannan su ne kabilan Efraim bisa ga kabilansu, daga Shutela, kabilar Shutelawa; daga Beker, kabilar Bekerawa; daga Tahan, kabilar Tahanawa.
36 And these are the sonnes of Shuthelah: of Eran the familie of the Eranites.
Waɗannan su ne kabilan Shutelawa, daga Eran, kabilar Eranawa.
37 These are the families of the sonnes of Ephraim after their nombers, two and thirtie thousand and fiue hundreth. these are the sonnes of Ioseph after their families.
Waɗannan su ne kabilan Efraim; jimillarsu ta kai 32,500. Waɗannan su ne kabilan Yusuf ta wurin kabilansu.
38 These are the sonnes of Beniamin after their families: of Bela came the familie of the Belaites: of Ashbel, the familie of the Ashbelites: of Ahiram, the familie of the Ahiramites:
Zuriyar Benyamin bisa ga kabilansu, daga Bela, kabilar Belawa; daga Ashbel, kabilar Ashbelawa; daga Ahiram, kabilar Ahiramawa;
39 Of Shupham, the familie of the Suphamites: of Hupham, the familie of the Huphamites.
daga Shufam, kabilar Shufamawa; daga Hufam, kabilar Hufamawa.
40 And the sonnes of Bela were Ard and Naaman: of Ard came the familie of the Ardites, of Naaman, the familie of the Naamites.
Zuriyar Bela daga Ard da Na’aman, daga Ard, kabilar Ardawa; daga Na’aman, kabilar Na’amawa;
41 These are the sonnes of Beniamin after their families, and their nombers, fiue and fourtie thousand and sixe hundreth.
Waɗannan su ne kabilan Benyamin, jimillarsu ta kai 45,600.
42 These are the sonnes of Dan after their families: of Shuham came the familie of the Shuhamites: these are the families of Dan after their housholdes.
Waɗannan su ne kabilan Dan bisa ga kabilarsu, daga Shuham, kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne kabilan Dan.
43 All the families of the Shuhamites were after their nombers, threescore and foure thousand, and foure hundreth.
Dukansu kabilan Shuhamawa ne, jimillarsu ta kai 64,400.
44 The sonnes of Asher after their families were: of Iimnah, the familie of the Iimnites: of Isui, the familie of the Isuites: of Beriah, the familie of the Berijtes.
Zuriyar Asher bisa ga kabilansu, daga Imna, kabilar Imnawa daga Ishbi, kabilar Ishbiyawa; daga Beriya, kabilar Beriyawa;
45 The sonnes of Beriah were, of Heber the familie of the Heberites: of Malchiel, the familie of the Malchielites.
daga zuriyar Beriya kuwa, daga Heber, kabilar Heberawa; daga Malkiyel, kabilar Malkiyelawa.
46 And the name of the daughter of Asher was Sarah.
(Asher yana da’ya mace da ake kira Sera.)
47 These are the families of the sonnes of Asher after their nombers, three and fifty thousand and foure hundreth.
Waɗannan su ne kabilan Asher; jimillarsu ta kai 53,400.
48 The sonnes of Naphtali, after their families were: of Iahzeel, the families of the Iahzeelites: of Guni, the familie of the Gunites.
Zuriyar Naftali bisa ga kabilansu, daga Yazeyel, kabilar Yazeyelawa; daga Guni, kabilar Guniyawa;
49 Of Iezer, the familie of the Izrites: of Shillem, the familie of the Shillemites.
daga Yezer, kabilar Yezerawa; daga Shillem, kabilar Shillemawa.
50 These are the families of Naphtali according to their housholdes, and their nomber, fiue and fourtie thousande and foure hundreth.
Waɗannan su ne kabilan Naftali, jimillarsu ta kai 45,400.
51 These are the nombers of the children of Israel: sixe hundreth and one thousand, seuen hundreth and thirtie.
Dukan jimillar mazan Isra’ila ta kai 601,730.
52 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
53 Vnto these the land shalbe deuided for an inheritance, according to the nomber of names.
“Ka rarraba musu ƙasar a matsayin gādo, bisa ga yawan kabila.
54 To many thou shalt giue the more inheritance, and to fewe thou shalt giue lesse inheritance: to euery one according to his nomber shalbe giuen his inheritance.
Ga ƙungiya mafi girma, ka ba ta rabo mafi girma; ga ƙaramar ƙungiya kuwa, ka ba ta ƙarami rabo; kowane zai karɓa rabonsa ga yawan mutanen da aka rubuta.
55 Notwithstanding, the land shalbe deuided by lot: according to the names of the tribes of their fathers they shall inherite:
Ka tabbatar an rarraba ƙasar ta wurin rabo. Abin da kowace ƙungiya ta gāda zai zama bisa ga sunayen kabilar kakanninta.
56 According to the lot shall the possession thereof be deuided betweene many and fewe.
Za a raba kowane gādo bisa ga rabo tsakanin manyan da ƙanana ƙungiyoyi.”
57 These also are the nobers of ye Leuites, after their families: of Gershon came ye familie of the Gershonites: of Kohath, ye familie of the Kohathites: of Merari, the familie of the Merarites.
Waɗannan su ne Lawiyawa da a ƙidaya bisa ga kabilansu, daga Gershom, kabilar Gershonawa; daga Kohat, kabilar Kohatawa; daga Merari, kabilar Merari.
58 These are the families of Leui, the familie of the Libnites: the familie of the Hebronites: the familie of the Mahlites: the familie of the Mushites: the familie of the Korhites: and Kohath begate Amram.
Waɗannan kuma su ne kabilan Lawiyawa, kabilar Libniyawa, kabilar Hebronawa, kabilar Maliyawa, kabilar Mushiyawa, kabilar Korayawa (Kohat shi ne kakan Amram;
59 And Amrams wife was called Iochebed the daughter of Leui, which was borne vnto Leui in Egypt: and she bare vnto Amram Aaron, and Moses, and Miriam their sister.
sunan matan Amram shi ne Yokebed, ita zuriyar Lawi ce, wadda aka haifa wa Lawiyawa a Masar. A wajen Amram kuwa ta haifi Haruna, Musa da kuma’yar’uwarsu Miriyam.
60 And vnto Aaron were borne Nadab, and Abihu, Eleazar, and Ithamar.
Haruna shi ne mahaifin Nadab, Abihu, Eleyazar da kuma Itamar.
61 And Nadab and Abihu dyed, because they offred strange fire before the Lord.
Amma Nadab da Abihu sun mutu sa’ad da suka miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji.)
62 And their nombers were three and twentie thousand, all males from a moneth old and aboue: for they were not nombred among the children of Israel, because there was none inheritance giuen them among the children of Israel.
Dukan’ya’yan Lawiyawa maza daga wata ɗaya zuwa gaba, jimillarsu ta kai 23,000. Ba a ƙidaya su tare da sauran Isra’ilawa ba, domin ba a ba su gādo tare da su ba.
63 These are the nombers of Moses and Eleazar the Priest which nombred the children of Israel in the plaine of Moab, neere Iorden, towarde Iericho.
Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eleyazar firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a filaye Mowab kusa da Urdun a hayen Yeriko.
64 And among these there was not a man of them, whome Moses and Aaron the Priest nobred, when they tolde the children of Israel in the wildernes of Sinai.
Ba ko ɗayansu da yake cikin waɗanda Musa da Haruna firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a Hamadar Sinai.
65 For the Lord said of them, They shall die in the wildernes: so there was not left a man of them, saue Caleb the sonne of Iephunneh, and Ioshua the sonne of Nun.
Gama Ubangiji ya riga ya gaya wa waɗancan Isra’ilawa cewa lalle za su mutu a hamada, kuma ba ko ɗayansu da ya rage, sai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.

< Numbers 26 >