< Nehemiah 5 >

1 Nowe there was a great crie of the people, and of their wiues against their brethren the Iewes.
To, sai maza da matansu suka tā da fara gunaguni mai tsanani a kan’yan’uwansu Yahudawa.
2 For there were that said, We, our sonnes and our daughters are many, therefore we take vp corne, that we may eate and liue.
Waɗansu suka ce, “Mu da’ya’yanmu maza da mata muna da yawa, muna bukatar hatsi domin mu ci mu rayu.”
3 And there were that saide, We must gage our landes, and our vineyardes, and our houses, and take vp corne for the famine.
Waɗansu kuwa suka ce, “Saboda yunwa mun jinginar da gonakinmu, da gonakin inabinmu, da gidajenmu don mu sami hatsi.”
4 There were also that said, We haue borowed money for the Kings tribute vpon our landes and our vineyardes.
Har illa yau waɗansu suka ce, “Mun ci bashin kuɗi don mu biya haraji a kan gonakinmu, da gonakin inabinmu.
5 And nowe our flesh is as the flesh of our brethren, and our sonnes as their sonnes: and lo, we bring into subiection our sonnes and our daughters, as seruants, and there be of our daughters nowe in subiection, and there is no power in our handes: for other men haue our landes and our vineyardes.
Ga shi kuwa, mu da su dangin juna ne,’ya’yanmu da nasu kuma ɗaya ne, duk da haka an tilasta mu mu sa’ya’yanmu mata da maza su zama bayi. Har ma an riga an bautar waɗansu daga cikin’ya’yanmu mata, amma ba mu da iko mu ce kome, domin gonakinmu da gonakin inabinmu suna a hannun waɗansu mutane.”
6 Then was I very angrie when I heard their crie and these wordes.
Sa’ad da na ji kukansu da waɗannan koke-koke, na husata ƙwarai.
7 And I thought in my minde, and I rebuked the princes, and the rulers, and saide vnto them, You lay burthens euery one vpon his brethren: and I set a great assemblie against them,
Na yi tunaninsu a zuciyata sa’an nan na zargi manyan gari da shugabanni. Na ce musu, “Kuna musguna wa’yan’uwanku ta wurin ba su rance da ruwa!” Saboda haka na kira babban taro gaba ɗaya don a magance wannan.
8 And I said vnto them, We (according to our abilitie) haue redeemed our brethren the Iewes, which were solde vnto the heathen: and will you sell your brethren againe, or shall they be solde vnto vs? Then helde they their peace, and could not answere.
Na ce, “Da dukan iyakar ƙoƙarinmu, mun fanshi’yan’uwanmu Yahudawan da aka sayar wa Al’ummai. Amma ga shi kuna sayar da’yan’uwanku ga Al’ummai, don kawai a sāke sayar mana da su!”
9 I said also, That which ye do, is not good. Ought ye not to walke in the feare of our God, for the reproche of the heathen our enemies?
Saboda haka na ci gaba na ce, “Abin da kuke yi a yanzu ba daidai ba ne. Bai kamata ku yi tafiya cikin tsoron Allahnmu don mu guji ba’ar Al’ummai abokan gābanmu ba?
10 For euen I, my brethren, and my seruants doe lende them money and corne: I pray you, let vs leaue off this burden.
Ni ma da’yan’uwana da kuma mutanena muna ba wa mutane bashin kuɗi da kuma hatsi. Sai mu daina sha’anin ba da rance da ruwa!
11 Restore, I pray you, vnto them this day their landes, their vineyardes, their oliues, and their houses, and remit the hundreth part of the siluer and of the corne, of the wine, and of the oyle that ye exact of them.
Yau sai ku mayar musu da gonakinsu, da gonakin inabinsu, da na zaitunsu, da gidajensu, da kashi ɗaya bisa ɗari na kuɗi, da na hatsi, da na ruwan inabi, da na mai, waɗanda kuka karɓa a wurinsu.”
12 Then said they, We will restore it, and will not require it of them: we will doe as thou hast said. Then I called the Priestes, and caused them to sweare, that they shoulde doe according to this promise.
Suka ce, “Za mu mayar musu, kuma ba za mu bukaci wani abu daga gare su ba. Za mu yi yadda ka faɗa.” Sai na tattara firistoci na kuma sa manyan gari da shugabanni su yi rantsuwa don su yi abin da suka yi alkawari.
13 So I shooke my lappe, and said, So let God shake out euery man that wil not perfourme this promise from his house, and from his labour: euen thus let him be shaken out, and emptied. And all the Cogregation said, Amen, and praised the Lord: and the people did according to this promise.
Na kuma kakkaɓe hannuna, na ce, “Duk wanda ya karya wannan alkawari, haka Allah zai kakkaɓe shi daga gidansa da aikinsa. Allah zai kakkaɓe shi, yă wofintar da shi!” Da jin wannan, sai dukan taron suka ce, “Amin,” suka kuma yabi Ubangiji. Mutane kuwa suka yi kamar yadda suka yi alkawari.
14 And from the time that the King gaue me charge to be gouernour in the lande of Iudah, from the twentieth yeere, euen vnto the two and thirtieth yeere of King Artahshashte, that is, twelue yeere, I, and my brethren haue not eaten the bread of the gouernour.
Ban da haka ma, daga shekara ta ashirin ta Sarki Artazerzes, sa’ad da aka naɗa ni in zama gwamnansu a ƙasar Yahuda, har zuwa shekara ta talatin da biyu na mulkinsa, shekara sha biyu ke nan, ko ni, ko’yan’uwana, ba wanda ya ci abincin da akan ba wa gwamna.
15 For the former gouernours that were before me, had bene chargeable vnto the people, and had taken of them bread and wine, besides fourtie shekels of siluer: yea, and their seruants bare rule ouer the people: but so did not I, because of the feare of God.
Amma gwamnonin farko, waɗanda suka riga ni, sun ɗaura wa mutane kaya mai nauyi suka karɓi shekel arba’in na azurfa daga gare su haɗe da abinci da kuma ruwan inabi. Har bayin masu mulki ma sun nawaya wa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda ina tsoron Allah.
16 But rather I fortified a portion in the worke of this wall, and we bought no lande, and all my seruants came thither together vnto the worke.
A maimakon haka, na miƙa kaina ga aiki a kan wannan katanga. Na tattara dukan mutanena a can don aikin; ba mu samar wa kanmu wata gona ba.
17 Moreouer there were at my table an hundreth and fiftie of the Iewes, and rulers, which came vnto vs from among the heathen that are about vs.
Bugu da ƙari, Yahudawa da shugabanni ɗari da hamsin suna ci daga teburina, haka ma waɗanda suka zo wurinmu daga ƙasashen da suke kewaye.
18 And there was prepared daily an oxe, and sixe chosen sheepe, and birdes were prepared for me, and within ten dayes wine for all in abundance. Yet for all this I required not the bread of the gouernour: for the bondage was grieuous vnto this people.
Kowace rana akan shirya mini saniya ɗaya, zaɓaɓɓun tumaki shida da waɗansu kaji, kuma kowace kwana goma akan tanadar da ruwan inabi na kowane iri a yalwace. Duk da haka, ban taɓa nemi a ba ni abincin da akan ba wa gwamna ba, domin wahala ta yi wa jama’a yawa.
19 Remember me, O my God, in goodnesse, according to all that I haue done for this people.
Ka tuna da ni, ka yi mini alheri, ya Allah, saboda dukan abubuwan da na yi saboda waɗannan mutane.

< Nehemiah 5 >