< Micah 3 >

1 And I sayd, Heare, I pray you, O heads of Iaakob, and yee princes of the house of Israel: should not ye knowe iudgement?
Sa’an nan na ce, “Ku kasa kunne, ku shugabannin Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila. Ya kamata ku san shari’a,
2 But they hate the good, and loue the euill: they plucke off their skinnes from them, and their flesh from their bones.
ku da kuke ƙin abu mai kyau kuke ƙaunar mugunta, ku da kuke feɗe mutanena kuke tuge nama daga ƙasusuwansu;
3 And they eate also the flesh of my people, and flay off their skinne from them, and they breake their bones, and chop them in pieces, as for the pot, and as flesh within the caldron.
ku da kuke cin naman mutanena, ku feɗe fatar jikinsu kuke kakkarya ƙasusuwansu, kuke yayyanka su gunduwa-gunduwa kamar naman da za a toya, kamar naman da za a sa a dafa.”
4 Then shall they crye vnto the Lord, but he will not heare them: he wil euen hide his face from them at that time, because they haue done wickedly in their workes.
Sa’an nan za su kira ga Ubangiji, amma ba zai amsa musu ba. A wannan lokaci zai ɓoye fuskarsa daga gare su saboda irin muguntar da suka yi.
5 Thus saith the Lord, Concerning the prophets that deceiue my people, and bite them with their teeth, and cry peace, but if a man put not into their mouthes, they prepare warre against him,
Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Game da annabawa masu ɓad da mutanena, in wani ya ciyar da su, sai su ce akwai ‘salama’ amma in bai ciyar da su ba, a shirye suke su kai masa hari.
6 Therefore night shalbe vnto you for a vision, and darkenesse shalbe vnto you for a diuination, and the sunne shall goe downe ouer the prophets, and the day shalbe darke ouer them.
Saboda haka dare yana zuwa a bisanku, ba tare da wahayi ba, kuma duhu, ba tare da duba ba. Rana za tă fāɗi wa annabawa, yini kuma zai zama musu duhu.
7 Then shall the Seers bee ashamed, and the southsayers confounded: yea, they shall all couer their lippes, for they haue none answere of God.
Masu gani za su ji kunya, masu duba kuma za su ji taƙaici. Dukansu za su rufe fuskokinsu gama ba amsa daga Allah.”
8 Yet notwithstanding I am full of power by the Spirite of the Lord, and of iudgement, and of strength to declare vnto Iaakob his transgression, and to Israel his sinne.
Amma game da ni, ina cike da iko ta wurin Ruhun Ubangiji da kuma adalci da ƙarfi, don a sanar da Yaƙub laifofinsa, ga Isra’ila kuma zunubinsa.
9 Heare this, I pray you, ye heades of the house of Iaakob, and princes of the house of Israel: they abhorre iudgement, and peruert all equitie.
Ku ji wannan, ku shugabannin gidan Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila, ku da kuke ƙyamar gaskiya, kuka karkatar duk abin da yake na gaskiya;
10 They build vp Zion with blood, and Ierusalem with iniquitie.
kuka gina Sihiyona ta wurin zub da jini, Urushalima kuma ta wurin mugunta.
11 The heads thereof iudge for rewardes, and the Priestes thereof teache for hyre, and the prophets thereof prophecie for money: yet wil they leane vpon the Lord, and say, Is not the Lord among vs? no euill can come vpon vs.
Hukunce-hukuncen shugabannin ƙasar na cin hanci ne, firistocinta kuma suna koyarwa don a biya su, annabawanta kuwa suna yin annabci don neman kuɗi. Duk da haka suna jingina a kan Ubangiji suna cewa, “Ba Ubangiji yana tare da mu ba? Ba bala’in da zai zo mana.”
12 Therefore shall Zion for your sake bee plowed as a field, and Ierusalem shalbe an heape, and the mountaine of the house, as the hye places of the forest.
Don haka, saboda ku, za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuma ta zama tarin juji, tudun haikali kuwa zai zama kurmin ƙayayyuwa.

< Micah 3 >