< Jonah 1 >

1 The worde of the Lord came also vnto Ionah the sonne of Amittai, saying,
Maganar Ubangiji ta zo wa Yunana ɗan Amittai cewa,
2 Arise, and goe to Nineueh, that great citie, and crye against it: for their wickednesse is come vp before mee.
“Tafi babban birnin nan Ninebe ka yi mata wa’azi, saboda muguntarta ta haura zuwa gabana.”
3 But Ionah rose vp to flee into Tarshish from the presence of the Lord, and went downe to Iapho: and he founde a ship going to Tarshish: so he payed the fare thereof, and went downe into it, that he might go with them vnto Tarshish, from the presence of the Lord.
Amma Yunana ya gudu daga Ubangiji ya nufi Tarshish. Ya gangara zuwa Yaffa, inda ya sami jirgin ruwa mai shirin tashi daga tashar. Bayan ya biya kuɗin tafiya, sai ya shiga jirgi ya kama hanya zuwa Tarshish don yă tsere wa Ubangiji.
4 But the Lord sent out a great winde into the sea, and there was a mightie tempest in the sea, so that the ship was like to be broken.
Sai Ubangiji ya aika da babban iska a bisan teku, hadiri ya tsananta ƙwarai har jirgin ya yi barazanar farfashewa.
5 Then the mariners were afraide, and cryed euery man vnto his God, and cast the wares that were in the ship, into the sea to lighten it of the: but Ionah was gone downe into the sides of the ship, and he lay downe, and was fast a sleepe.
Dukan matuƙan jirgin suka tsorata, kowannensu kuma ya yi kuka ga allahnsa, suka kuma jefar da kayan jirgi a cikin teku domin su rage nauyin jirgin. Ana cikin haka, ashe, Yunana ya sauka can ƙarƙashin jirgi ya je ya kwanta, yana ta sharar barcinsa.
6 So the shipmaster came to him, and saide vnto him, What meanest thou, O sleeper? Arise, call vpon thy God, if so be that God wil thinke vpon vs, that we perish not.
Sai kyaftin ɗin ya je wajensa ya ce masa, “Don me kake barci? Tashi ka kira bisa ga allahnka! Mai yiwuwa yă ji mu, yă cece mu don kada mu hallaka.”
7 And they saide euery one to his fellowe, Come, and let vs cast lottes, that we may know, for whose cause this euill is vpon vs. So they cast lottes, and the lot fell vpon Ionah.
Matuƙan jirgin suka ce wa juna, “Ku zo, mu jefa ƙuri’a mu ga wa ke da alhakin wannan masifa.” Sai suka jefa ƙuri’a, ƙuri’ar kuwa ta fāɗa a kan Yunana.
8 Then said they vnto him, Tell vs for whose cause this euill is vpon vs? what is thine occupation? and whence commest thou? which is thy countrey? and of what people art thou?
Saboda haka suka tambaye shi suka ce, “Yanzu, gaya mana, dalilin da ya sa wannan masifa ta zo mana? Mene ne aikinka? Daga ina ka fito? Ina ne ƙasarka? Daga wacce kabila ce ka fito?”
9 And he answered them, I am an Ebrewe, and I feare the Lord God of heauen, which hath made the sea, and the dry lande.
Sai ya amsa, “Ni mutumin Ibraniyawa ne, ina kuma bauta wa Ubangiji Allah na sama, wanda ya yi teku da tuddai.”
10 Then were the men exceedingly afrayde, and said vnto him, Why hast thou done this? (for the men knewe, that he fled from the presence of the Lord, because he had tolde them)
Sai matuƙan jirgin suka tsorata ƙwarai, suka ce masa, “Wane irin mugun abu ne ka aikata haka?” (Sun gane cewa yana gudu ne daga wurin Ubangiji, domin ya riga ya faɗa musu.)
11 Then saide they vnto him, What shall we doe vnto thee, that the sea may be calme vnto vs? (for the sea wrought and was troublous)
Sai tekun ya daɗa rikicewa. Sai suka tambaye shi, “Me za mu yi da kai domin tekun yă daina hauka?”
12 And he said vnto them, Take me, and cast me into the sea: so shall the sea be calme vnto you: for I knowe that for my sake this great tempest is vpon you.
Ya amsa musu ya ce, “Ku ɗauke ni ku jefa a cikin teku, tekun zai kwanta. Na san cewa laifina ne ya jawo wannan babban hadirin da ya auka muku.”
13 Neuerthelesse, the men rowed to bring it to the lande, but they coulde not: for the sea wrought, and was troublous against them.
Maimakon mutanen su yi haka, sai suka yi ƙoƙari su tura jirgin ruwan zuwa bakin teku. Amma ba su iya ba, saboda iskar ta sa tekun ya yi ta ƙara hauka.
14 Wherefore they cryed vnto the Lord, and said, We beseech thee, O Lord, we beseech thee, let vs not perish for this mans life, and lay not vpon vs innocent blood: for thou, O Lord, hast done, as it pleased thee.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji suka ce, “Ya Ubangiji, in ka yarda kada ka bar mu mu mutu saboda ran mutumin nan. Kada ka yi mana hukuncin masu kisankai, gama kai ne, ya Ubangiji, ka ga ya gamshe ka.”
15 So they tooke vp Ionah, and cast him into the sea, and the sea ceased from her raging.
Sa’an nan suka ɗauki Yunana suka jefar da shi daga jirgin, sai tekun ya kwanta.
16 Then the men feared the Lord exceedingly, and offered a sacrifice vnto the Lord, and made vowes.
Ganin haka sai mutanen suka cika da tsoron Ubangiji, suka kuma miƙa wa Ubangiji hadaya, suka yi wa’adi da shi.
17 Nowe the Lord had prepared a great fish to swallowe vp Ionah: and Ionah was in the belly of the fish three dayes, and three nightes.
Amma Ubangiji ya tanada wani babban kifi da zai haɗiye Yunana, Yunana kuwa ya yi yini uku da dare uku a ciki cikin kifin.

< Jonah 1 >