< Leviticus 8 >

1 Afterwarde the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Take Aaron and his sonnes with him, and the garments and the anointing oyle, and a bullocke for the sinne offring, and two rammes, and a basket of vnleauened bread,
“Kawo Haruna da’ya’yansa maza, ka ɗauki rigunansu, man keɓewa, bijimi domin hadaya don zunubi,’yan raguna biyu da kuma kwandon da yake da burodi marar yisti,
3 And assemble all the company at the doore of the Tabernacle of the Congregation.
ka kuma tara dukan jama’a a ƙofar Tentin Sujada.”
4 So Moses did as the Lord had commanded him, and the companie was assembled at the doore of the Tabernacle of the Congregation.
Sai Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi, jama’a kuwa suka taru a ƙofar Tentin Sujada.
5 Then Moses said vnto the company, This is the thing which the Lord hath commanded to doe.
Sai Musa ya ce wa jama’ar, “Ga abin da Ubangiji ya umarta a yi.”
6 And Moses brought Aaron and his sonnes, and washed them with water,
Sa’an nan Musa ya kawo Haruna da’ya’yansa maza gaba, ya kuma wanke su da ruwa.
7 And put vpon him the coate, and girded him with a girdle, and clothed him with the robe, and put the Ephod on him, which he girded with the broydred garde of the Ephod, and bounde it vnto him therewith.
Ya sa wa Haruna taguwa, ya ɗaura igiya kewaye da shi, ya sa masa riga, ya sa masa efod. Ya kuma ɗaura masa efod wanda aka yi masa saƙar gwaninta.
8 After he put the brest plate thereon, and put in the breast plate the Vrim and the Thummim.
Ya sa masa ƙyallen maƙalawa a ƙirji, ya kuma sa Urim da Tummim a ƙyallen maƙalawa a ƙirjin.
9 Also he put the miter vpon his head, and put vpon the miter on the fore front the golden plate, and the holy crowne, as the Lord had commanded Moses.
Sai ya naɗa masa rawani, daga gaban rawanin ya sa allon zinariya, wato, kambi tsattsarka, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.
10 (Nowe Moses had taken the anointing oyle, and anoynted the Tabernacle, and al that was therein, and sanctified them,
Sa’an nan Musa ya ɗauki man keɓewa ya keɓe tabanakul da kuma kowane abin da yake cikinsa, ta haka ya tsarkake su.
11 And sprinkled thereof vpon the altar seuen times, and anointed the altar and all his instruments, and the lauer, and his foote, to sanctifie them)
Ya yayyafa mai a kan bagade sau bakwai, yana keɓe bagade da dukan kayayyaki, da daro, da abin da yake tsaya a kai, don yă tsarkake su.
12 And he powred of the anointing oyle vpon Aarons head, and anointed him, to sanctifie him.
Ya zuba man keɓewa a kan Haruna, ya kuma keɓe shi don yă tsarkake shi.
13 After, Moses brought Aarons sonnes, and put coates vpon them, and girded them with girdles, and put bonets vpon their heades, as the Lord had commanded Moses.
Sa’an nan ya kawo’ya’yan Haruna maza, ya sa musu taguwoyi, ya ɗaɗɗaura igiyoyi kewaye da su, ya kuma sa musu huluna yadda Ubangiji ya umarce shi.
14 Then he brought the bullocke for the sinne offring, and Aaron and his sonnes put their handes vpon the head of the bullocke for the sinne offring.
Sa’an nan ya miƙa bijimi domin hadaya don zunubi, sai Haruna da’ya’yansa suka ɗibiya hannuwansu a bijimin.
15 And Moses slew him, and tooke the blood, which he put vpon the hornes of the Altar roud about with his finger, and purified the altar, and powred the rest of the blood at the foote of ye altar: so he sanctified it, to make reconciliation vpon it.
Musa ya yanka bijimin ya ɗauki jinin, ya sa yatsarsa ya zuba a dukan ƙahonin bagade don yă tsarkake bagaden. Ya zuba sauran jinin a gindin bagade. Ta haka ya tsarkake shi don yă yi kafara dominsa.
16 Then he tooke all the fatte that was vpon the inwardes, and the kall of the liuer and the two kidneis, with their fat, which Moses burned vpon the Altar.
Musa ya ɗebo dukan kitsen da yake kewaye da kayan ciki, da kuma wanda ya rufe hanta, da ƙodojin, da kuma kitsensu, ya kuma ƙone su a kan bagade.
17 But the bullocke and his hide, and his flesh, and his doung, hee burnt with fire without the host as the Lord had commanded Moses.
Amma bijimin da fatarsa da namansa da kuma ƙashinsa ya ƙone su a bayan sansani, yadda Ubangiji ya umarce shi.
18 Also hee brought the ram for the burnt offring, and Aaron and his sonnes put their hands vpon the head of the ramme.
Sa’an nan ya miƙa ɗan rago domin hadaya ta ƙonawa, sai Haruna da’ya’yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan ɗan rago.
19 So Moses killed it, and sprinkled the blood vpon the Altar round about,
Sa’an nan Musa ya yanka ɗan ragon, ya kuma yayyafa jinin a kowane gefe na bagaden.
20 And Moses cut the ram in pieces, and burnt the head with the pieces, and the fat,
Ya yanka ragon gunduwa-gunduwa ya ƙone kan, ya kuma ƙone gunduwa-gunduwan da kitsen.
21 And washed the inwardes and the legges in water: so Moses burnt the ram euery whit vpon ye Altar: for it was a burnt offring for a sweete sauour, which was made by fire vnto the Lord, as the Lord had commanded Moses.
Ya wanke kayan cikin da ƙafafun a ruwa, ya kuma ƙone dukan ragon a bisa bagade kamar hadaya ta ƙonawa, mai daɗin ƙanshi, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
22 After, he brought the other ram, the ram of consecrations, and Aaron and his sonnes layed their handes vpon the head of the ram,
Sai ya miƙa ɗayan ɗan ragon, ɗan ragon naɗin, sai Haruna da’ya’yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan ɗan ragon.
23 Which Moses slewe, and tooke of the blood of it, and put it vpon the lappe of Aarons right eare, and vpon the thumbe of his right hand, and vpon the great toe of his right foote.
Musa kuwa ya yanka ɗan ragon ya ɗibi jinin ya sa leɓatun kunnen dama na Haruna, ya kuma sa a babbar yatsarsa ta hannun dama da kuma a babbar yatsar ƙafarsa ta dama.
24 Then Moses brought Aarons sonnes, and put of the blood on the lap of their right eares, and vpon the thumbes of their right handes, and vpon the great toes of their right feete, and Moses sprinckled the rest of the blood vpon the Altar round about.
Musa ya kuma kawo’ya’yan Haruna gaba, ya sa jini a leɓatun kunnuwansu na dama, ya kuma sa a manyan yatsotsinsu na hannun dama da kuma a manyan yatsotsinsu na ƙafafunsu na dama. Sa’an nan ya yayyafa jinin a kowane gefen bagade.
25 And he tooke the fat and the rumpe and all the fat that was vpon the inwards, and the kall of the liuer, and the two kidneis with their fat, and the right shoulder.
Ya ɗibi kitsen, da wutsiya mai kitse, da kuma dukan kitsen da ke kewaye da kayan ciki, da wanda ya rufe hanta, ƙodoji biyu da kitsensu da kuma cinya ta dama.
26 Also he tooke of ye basket of ye vnleauened bread that was before the Lord, one vnleauened cake and a cake of oiled bread, and one wafer, and put them on the fat, and vpon the right shoulder.
Sa’an nan daga cikin kwandon burodi marar yisti wanda yake a gaban Ubangiji, ya ɗauko dunƙulen burodi, da kuma guda da aka yi da mai, da kuma ƙosai; ya sa waɗannan a sassan kitsen, da kuma a cinya ta dama.
27 So hee put all in Aarons handes, and in his sonnes handes, and shooke it to and from before the Lord.
Ya sa waɗannan a hannuwan Haruna da’ya’yansa, suka kuma kaɗa su a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa.
28 After, Moses tooke the out of their hands, and burnt them vpon the altar for a burnt offring: for these were consecrations for a sweete sauour which were made by fire vnto the Lord.
Sa’an nan Musa ya karɓe su daga hannuwansu ya ƙone a bagade a bisa hadaya ta ƙonawa a matsayin hadaya ta naɗi, mai daɗin ƙanshi, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
29 Likewise Moses tooke the breast of the ram of consecrations, and shooke it to and from before the Lord: for it was Moses portion, as the Lord had commanded Moses.
Ya kuma ɗauki ƙirjin; rabon Musa na ɗan ragon naɗi, ya kaɗa shi a gaban Ubangiji, a matsayin hadaya ta kaɗawa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
30 Also Moses tooke of the anointing oyle, and of the blood which was vpon the Altar, and sprinkled it vpon Aaron, vpon his garments, and vpon his sonnes, and on his sonnes garments with him: so hee sanctified Aaron, his garments, and his sonnes, and his sonnes garments with him.
Sai Musa ya ɗibi man keɓewa da jini daga bagade, ya yayyafa su a kan Haruna da rigunansa, da kuma a kan’ya’yansa da rigunansu, don yă tsarkake Haruna da rigunansa da kuma’ya’yansa da rigunansu.
31 Afterward Moses saide vnto Aaron and his sonnes, Seethe the flesh at the doore of the Tabernacle of the Congregation, and there eate it with the bread that is in the basket of consecrations, as I commanded, saying, Aaron and his sonnes shall eate it,
Sai Musa ya ce wa Haruna da’ya’yansa maza, “Ku dafa naman a ƙofar Tentin Sujada, ku kuma ci shi a can tare da burodi daga kwandon naɗi, yadda na umarta, cewa, ‘Haruna da’ya’yansa maza za su ci shi.’
32 But that which remaineth of the flesh and of the bread, shall ye burne with fire.
Sa’an nan ku ƙone sauran naman da kuma burodin.
33 And ye shall not depart from the doore of the Tabernacle of the Congregation seuen dayes, vntill the dayes of your consecrations bee at an ende: for seuen dayes, saide the Lord, shall hee consecrate you,
Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada har kwana bakwai, sai ranakun naɗi suka cika, gama naɗinku zai ɗauki kwana bakwai.
34 As hee hath done this day: so the Lord hath commanded to doe, to make an atonement for you.
Abin da aka yi a yau umarni ne daga Ubangiji don yin kafara saboda ku.
35 Therefore shall yee abide at the doore of the Tabernacle of the Congregation day and night, seuen dayes, and shall keepe the watch of the Lord, that ye dye not: for so I am commanded.
Dole ku kasance a ƙofar Tentin Sujada dare da rana har kwana bakwai, ku kuma yi abin da Ubangiji yake bukata, don kada ku mutu; gama abin da aka umarce ni ke nan.”
36 So Aaron and his sonnes did all thinges which the Lord had commanded by the hand of Moses.
Saboda haka Haruna da’ya’yansa maza suka yi kome da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.

< Leviticus 8 >