< Exodus 1 >

1 Now these are the names of the children of Israel, which came into Egypt (euery man and his housholde came thither with Iaakob)
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
2 Reuben, Simeon, Leui, and Iudah,
Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
3 Issachar, Zebulun, and Beniamin,
Issakar, Zebulun da Benyamin;
4 Dan, and Naphtali, Gad, and Asher.
Dan da Naftali; Gad da Asher.
5 So al the soules, that came out of the loines of Iaakob, were seuentie soules: Ioseph was in Egypt already.
Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
6 Nowe Ioseph died and all his brethren, and that whole generation.
Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
7 And the children of Israel brought foorth fruite and encreased in aboundance, and were multiplied, and were exceeding mightie, so that the land was full of them.
amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
8 Then there rose vp a newe King in Egypt, who knewe not Ioseph.
Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
9 And he sayde vnto his people, Beholde, the people of the children of Israel are greater and mightier then we.
Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
10 Come, let vs worke wisely with them, least they multiplie, and it come to passe, that if there be warre, they ioyne them selues also vnto our enemies, and fight against vs, and get them out of the land.
Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
11 Therefore did they set taskemasters ouer them, to keepe the vnder with burdens: and they built the cities Pithom and Raamses for the treasures of Pharaoh.
Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
12 But the more they vexed them, the more they multiplied and grewe: therefore they were more grieued against the children of Israel.
Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
13 Wherefore the Egyptians by crueltie caused the children of Israel to serue.
ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
14 Thus they made them weary of their liues by sore labour in clay and in bricke, and in al worke in the fielde, with all maner of bondage, which they layde vpon them most cruelly.
Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
15 Moreouer the King of Egypt commanded ye midwiues of the Ebrewe women, (of which the ones name was Shiphrah, and the name of the other Puah)
Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
16 And sayde, When ye doe the office of a midwife to the women of the Ebrewes, and see them on their stooles, if it be a sonne, then yee shall kill him: but if it be a daughter, then let her liue.
“Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
17 Notwithstanding ye midwiues feared God, and did not as the King of Egypt commanded them, but preserued aliue the men children.
Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
18 Then the King of Egypt called for the midwiues, and sayde vnto them, Why haue yee done thus, and haue preserued aliue the men children?
Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
19 And the midwiues answered Pharaoh, Because the Ebrewe women are not as the women of Egypt: for they are liuely, and are deliuered yer the midwife come at them.
Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
20 God therefore prospered the midwiues, and the people multiplied and were very mightie.
Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
21 And because ye midwiues feared God, therefore he made them houses.
Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
22 Then Pharaoh charged all his people, saying, Euery man childe that is borne, cast yee into the riuer, but reserue euery maide childe aliue.
Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”

< Exodus 1 >