< Leviticus 22 >

1 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Speake vnto Aaron, and to his sonnes, that they be separated from the holy thinges of the children of Israel, and that they pollute not mine holy name in those things, which they hallowe vnto me: I am the Lord.
“Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, su lura da tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka keɓe gare ni da bangirma, saboda ba za su ƙazantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Ubangiji.
3 Say vnto them, Whosoeuer he be of all your seede among your generations after you, that toucheth the holy things which the children of Israel hallowe vnto the Lord, hauing his vncleannesse vpon him, euen that person shall be cut off from my sight: I am the Lord.
“Faɗa musu cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, in wani zuriyarku ya ƙazantu, duk da haka ya kusaci tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka keɓe ga Ubangiji, dole a raba wannan mutum daga gabana. Ni ne Ubangiji.
4 Whosoeuer also of the seede of Aaron is a leper, or hath a running issue, he shall not eate of the holy things vntill he be cleane: and who so toucheth any that is vncleane, by reason of the dead, or a man whose issue of seede runneth from him,
“‘In zuriyar Haruna yana da kuturu, ko mai ɗiga, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa ba, sai lokacin da ya tsarkaka. Duk wanda ya taɓa wani abu marar tsarki na mamaci, ko wanda maniyyinsa yake ɗiga,
5 Or the man that toucheth any creeping thing, whereby he may be made vncleane, or a man, by whom he may take vncleannesse, whatsoeuer vncleannesse he hath,
da duk kuma wanda ya taɓa wani abu mai rarrafe wanda yake ƙazantarwa, ko kuwa wani mutum mai ƙazanta,
6 The person that hath touched such, shall therefore be vncleane vntill the euen, and shall not eat of ye holy things, except he haue washed his flesh with water.
duk mutumin da ya taɓa kowane irin abu haka, zai ƙazantu har yamma, ba kuwa zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwan nan ba, sai ya yi wanka tukuna.
7 But when the Sunne is downe, hee shalbe cleane, and shall afterward eate of the holy things: for it is his foode.
Sa’ad da rana ta fāɗi, zai zama tsarkakakke, bayan wannan kuwa zai iya cin tsarkakakkun hadayu, gama abincinsa ne.
8 Of a beast that dyeth, or is rent with beasts, whereby he may be defiled, hee shall not eate: I am the Lord.
Kada yă ci wani abin da ya mutu mushe, ko wanda namun jeji suka yayyaga, don kada yă ƙazantar da kansa. Ni ne Ubangiji.
9 Let them keepe therefore mine ordinance, least they beare their sinne for it, and die for it, if they defile it: I the Lord sanctifie them.
“‘Firistoci za su kiyaye umarnaina don kada su yi laifi su mutu saboda sun rena su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da su masu tsarki.
10 There shall no stranger also eate of the holie thing, neither the ghest of the Priest, neither shall an hired seruant eat of the holie thing:
“‘Duk wanda ba daga cikin iyalin firistoci ba, ko da yake yana zama tare da su, ko kuwa an ɗauke shi yana yin musu aiki, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun hadayun ba.
11 But if the Priest bye any with money, he shall eate of it, also he that is borne in his house: they shall eate of his meate.
Amma in firist ya sayi bawa da kuɗi, ko kuwa in an haifi bawan a gidansa, wannan bawan zai iya cin tsattsarkan abincin.
12 If the Priests daughter also be maried vnto a stranger, she may not eate of the holy offrings.
In’yar firist ta auri wani da ba firist ba, ba za tă ci wani tsarkakakkun sadaka ba.
13 Notwithstanding if the Priests daughter be a widowe or diuorced, and haue no childe, but is returned vnto her fathers house shee shall eate of her fathers bread, as she did in her youth but there shall no stranger eate thereof.
Amma idan’yar firist ta zama gwauruwa ko sakakkiya, ba ta da’ya’ya, ta kuwa dawo don tă zauna a gidan mahaifinta kamar matashiya, za tă iya cin abincin.
14 If a man eate of the holie thing vnwittingly, he shall put the fift part thereunto, and giue it vnto the Priest with the halowed thing.
“‘In wani ya ci tsarkakakken abinci cikin kuskure, dole yă maido wa firist hadayar, yă kuma ƙara kashi ɗaya bisa biyar na tamanin abin.
15 So they shall not defile the holy things of the children of Israel, which they offer vnto the Lord,
Firist ɗin ba zai ƙasƙantar da tsarkakakkun hadayun da Isra’ilawa suka kawo ga Ubangiji
16 Neither cause the people to beare the iniquitie of their trespas, while they eate their holy thing: for I the Lord do halowe them.
ta wurin barinsu su ci tsarkakakkun hadayu, ta yin haka su jawo wa kansu laifin da zai bukaci biya ba. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.’”
17 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
18 Speake vnto Aaron, and to his sonnes, and to all the children of Israel, and say vnto them, Whosoeuer he be of the house of Israel, or of the strangers in Israel, that will offer his sacrifice for all their vowes, and for all their free offrings, which they vse to offer vnto the Lord for a burnt offring,
“Yi wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa magana ka ce musu, ‘In waninku, ko mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a Isra’ila, ya kawo kyauta don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko don yă cika alkawari, ko kuwa a matsayin hadaya ta yardar rai,
19 Yee shall offer of your free minde a male without blemish of the beeues, of the sheepe, or of the goates.
dole ku miƙa dabba namiji marar lahani, daga shanu, tumaki, ko awaki, domin yă zama yardajje a madadinku.
20 Ye shall not offer any thing that hath a blemish: for that shall not be acceptable for you.
Kada ku kawo wani abu mai lahani, domin ba zai zama yardajje ba a madadinku.
21 And whosoeuer bringeth a peace offring vnto ye Lord to accomplish his vowe, or for a free offring, of the beeues, or of the sheepe, his free offring shall bee perfect, no blemish shalbe in it.
Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta salama daga garken shanu, ko na tumaki, ga Ubangiji don yă cika wani alkawari na musamman, ko hadaya ta yardar rai, dole yă zama marar lahani, ko tabo, don yă zama yardajje.
22 Blinde, or broken, or maimed, or hauing a wenne, or skiruie, or skabbed: these shall yee not offer vnto the Lord nor make an offring by fire of these vpon the altar of the Lord.
Kada ku miƙa wa Ubangiji dabbobi makafi, ko naƙasassu, ko masu gundumi, ko masu ɗiga, ko masu susa, ko masu kirci. Kada ku sa wani daga cikin waɗannan a bisa bagade a matsayin hadaya, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
23 Yet a bullocke, or a sheepe that hath any member superfluous, or lacking, such mayest thou present for a free offring, but for a vowe it shall not be accepted.
Za ku iya miƙa hadaya ta yardar rai da maraƙi, ko tunkiya mai naƙasa, ko marar cikakken lafiya, amma ba za tă zama yardajje don cika alkawarin da aka yi ba.
24 Ye shall not offer vnto ye Lord that which is bruised or crusshed, or broken, or cut away, neither shall ye make an offring thereof in your land,
Ba za ku miƙa wa Ubangiji dabbar da lunsayinta yake da ƙujewa, ko dandaƙewa, ko yagewa, ko yankewa ba.
25 Neither of ye hand of a strager shall ye offer ye bread of your God of any of these, because their corruption is in them, there is a blemish in them: therefore shall they not be accepted for you.
Ba za ku kuma karɓi irin waɗannan dabbobi daga hannun baƙi ku miƙa su a matsayin abinci ga Allahnku ba. Ba za su zama yardajje a madadinku ba, domin sun naƙasa, suna kuma da lahani.’”
26 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
27 When a bullocke, or a sheepe, or a goate shall be brought foorth, it shalbe euen seuen daies vnder his damme: and from the eight day forth, it shalbe accepted for a sacrifice made by fire vnto the Lord.
“Sa’ad da aka haifi ɗan maraƙi, tunkiya, ko akuya, sai yă kasance da mahaifiyarsa kwana bakwai. Daga rana ta takwas zuwa gaba, zai zama yardajje hadaya, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
28 As for the cowe or the ewe, yee shall not kill her, and her yong both in one day.
Kada a yanka saniya, ko tunkiya da ɗanta rana ɗaya.
29 So when ye will offer a thanke offring vnto the Lord, ye shall offer willingly.
“Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, ku miƙa ta a yadda za tă zama yardajje a madadinku.
30 The same day it shalbe eaten, yee shall leaue none of it vntill the morowe: I am the Lord.
Dole a ci hadayar a ranar; kada a bar saura sai da safe. Ni ne Ubangiji.
31 Therefore shall ye keepe my commandements and do them: for I am the Lord.
“Ku kiyaye dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.
32 Neither shall ye pollute mine holy Name, but I will be halowed among the children of Israel. I the Lord sanctifie you,
Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole Isra’ilawa su gane Ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji, wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka
33 Which haue brought you out of the land of Egypt, to be your God: I am the Lord.
da kuma wanda ya fitar da ku daga Masar don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”

< Leviticus 22 >