< Leviticus 19 >

1 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Speake vnto all the Congregation of the children of Israel, and say vnto them, Ye shalbe holy, for I the Lord your God am holy.
“Yi wa taron jama’ar Isra’ila gaba ɗaya magana, ka ce musu, ‘Ku zama masu tsarki, domin Ni, Ubangiji Allahnku, mai tsarki ne.
3 Yee shall feare euery man his mother and his father, and shall keepe my Sabbaths: for I am the Lord your God.
“‘Dole kowannenku yă girmama mahaifiyarsa da mahaifinsa, dole kuma ku kiyaye Asabbacina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
4 Ye shall not turne vnto idoles, nor make you molten gods: I am the Lord your God.
“‘Kada ku juyo ga gumaka, ko ku yi wa kanku allolin da aka yi zubi da ƙarfe. Ni ne Ubangiji Allahnku.
5 And when yee shall offer a peace offering vnto the Lord, ye shall offer it freely.
“‘Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, ku miƙa ta yadda za tă karɓu a madadinku.
6 It shall be eaten the day yee offer it, or on the morowe: and that which remaineth vntill the third day, shalbe burnt in the fire.
Za a ci ta a ranar da kuka miƙa ta, ko kuwa a kashegarin; duk abin da ya rage har kwana ta uku dole a ƙone shi.
7 For if it be eaten the third day, it shall be vncleane, it shall not be accepted.
In aka ci ta a rana ta uku, marar tsabta ce, ba kuma za a karɓe ta ba.
8 Therefore he that eateth it, shall beare his iniquitie, because he hath defiled the halowed thing of the Lord, and that person shalbe cut off from his people.
Duk wanda ya ci ta zai zama da laifi domin ya ƙazantar da abin da yake da tsarki ga Ubangiji, dole a raba mutumin nan da mutanensa.
9 When yee reape the haruest of your land, ye shall not reape euery corner of your field, neither shalt thou gather the glainings of thy haruest.
“‘Sa’ad da kuka yi girbin amfanin gonarku, kada ku girbe har zuwa gefen gonar, ko ku yi kalan girbinku.
10 Thou shalt not gather the grapes of thy vineyarde cleane, neyther gather euery grape of thy vineyarde, but thou shalt leaue them for the poore and for the straunger: I am the Lord your God.
Kada ku koma gonar inabinku kuna kala, ko ku tattara’ya’yan inabin da suka fāffāɗi. Ku bar su domin matalauta da kuma baƙi. Ni ne Ubangiji Allahnku.
11 Ye shall not steale, neither deale falsely, neither lie one to another.
“‘Kada ku yi sata. “‘Kada ku yi ƙarya. “‘Kada ku ruɗe juna.
12 Also yee shall not sweare by my name falsely, neither shalt thou defile the name of thy God: I am the Lord.
“‘Kada ku rantse bisa ƙarya da sunana, ta haka har ku ƙasƙantar da sunan Allahnku. Ni ne Ubangiji.
13 Thou shalt not do thy neighbour wrong, neither rob him. The workemans hire shall not abide with thee vntil the morning.
“‘Kada ku zalunci maƙwabcinku, ko ku yi masa ƙwace. “‘Kada ku riƙe albashin ma’aikaci yă kwana.
14 Thou shalt not curse the deafe, neither put a stumbling blocke before the blinde, but shalt feare thy God: I am the Lord.
“‘Kada ku zagi kurma, ko ku sa abin tuntuɓe a gaban makaho, amma ku ji tsoron Allahnku. Ni ne Ubangiji.
15 Ye shall not doe vniustly in iudgement. Thou shalt not fauour the person of the poore, nor honour the person of the mightie, but thou shalt iudge thy neighbour iustly.
“‘Kada ku yi rashin adalci cikin shari’a; kada ku nuna sonkai ga matalauci, ko ku goyi bayan mai arziki, amma ku shari’anta maƙwabci cikin gaskiya.
16 Thou shalt not walke about with tales among thy people. Thou shalt not stand against the blood of thy neighbour: I am the Lord.
“‘Kada ku yi ta yawo kuna yaɗa ƙarya a cikin mutanenku. “‘Kada ku yi wani abin da zai sa ran maƙwabcinku cikin hatsari. Ni ne Ubangiji.
17 Thou shalt not hate thy brother in thine heart, but thou shalt plainely rebuke thy neighbour, and suffer him not to sinne.
“‘Kada ka yi ƙiyayyar ɗan’uwanka a zuciya. Ka tsawata wa maƙwabcinka da gaske don kada ka sami rabo cikin laifinsa.
18 Thou shalt not auenge, nor be mindful of wrong against ye childre of thy people, but shalt loue thy neighbour as thy selfe: I am the Lord.
“‘Kada ka nemi yin ramuwa, ko ka riƙe wani cikin mutanenka a zuciya, amma ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka. Ni ne Ubangiji.
19 Yee shall keepe mine ordinances. Thou shalt not let thy cattel gender with others of diuers kindes. Thou shalt not sowe thy fielde with mingled seede, neyther shall a garment of diuers thinges, as of linen and wollen come vpon thee.
“‘Ku kiyaye farillaina. “‘Kada ku sa dabbobin da ba iri ɗaya ba su yi barbara. “‘Kada ku yi shuki iri biyu a gonarku. “‘Kada ku sa rigar da aka saƙa da yadi iri biyu.
20 Whosoeuer also lyeth and medleth with a woman that is a bonde mayde, affianced to a husband, and not redeemed, nor freedome giuen her, she shalbe scourged, but they shall not die, because she is not made free.
“‘In wani ya kwana da mace wadda take baiwa, wadda aka yi wa wani alkawari amma bai fanshe ta ba, ko kuwa ba a’yantar da ita ba, dole a yi hukuncin da ya dace. Duk da haka ba za a kashe su ba, domin ba a’yantar da ita ba.
21 And he shall bring for his trespasse offring vnto the Lord, at the doore of the Tabernacle of the Congregation, a ramme for a trespasse offering.
Dole mutumin da ya kwana da ita yă kawo rago a ƙofar Tentin Sujada domin hadaya don laifi ga Ubangiji.
22 Then the Priest shall make an atonement for him with the ramme of the trespasse offering before the Lord, concerning his sinne which he hath done, and pardon shalbe giuen him for his sinne which he hath committed.
Da ragon hadaya don laifin ne firist zai yi kafara saboda mutumin a gaban Ubangiji saboda zunubin da ya yi, za a kuwa gafarta zunubinsa.
23 Also when ye shall come into the land, and haue planted euery tree for meate, ye shall count the fruite thereof as vncircumcised: three yeere shall it be vncircumcised vnto you, it shall not be eaten:
“‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar kuka kuma shuka kowane irin itace mai’ya’ya na ci, ku ɗauki’ya’yan itatuwan nan a matsayi an hana ku ci. Shekara uku za ku ɗauka a matsayi an hana ku, ba za ku ci su ba.
24 But in the fourth yere all the fruite thereof shalbe holy to the praise of the Lord.
A shekara ta huɗu, dukan’ya’yansu za su zama tsarkakakku, hadaya ta yabo ga Ubangiji.
25 And in the fifth yeere shall ye eate of the fruite of it that it may yeelde to you the encrease thereof: I am the Lord your God.
Amma a shekara ta biyar, za ku iya cin’ya’yan itatuwan. Ta haka girbinku zai ƙaru. Ni ne Ubangiji Allahnku.
26 Ye shall not eat the flesh with the blood, ye shall not vse witchcraft, nor obserue times.
“‘Kada ku ci wani abinci tare da jini a cikinsa. “‘Kada ku yi duba ko sihiri.
27 Ye shall not cut rounde the corners of your heades, neither shalt thou marre the tuftes of thy beard.
“‘Ba za ka aske gefe-gefe na gashin kanka ba, ko ku aske gemunku.
28 Ye shall not cut your flesh for the dead, nor make any print of a marke vpon you: I am the Lord,
“‘Kada ku tsattsaga jikunanku saboda matattu, ba kuwa za ku yi wa kanku zāne-zāne a jiki ba. Ni ne Ubangiji.
29 Thou shalt not make thy daughter common, to cause her to be a whore, least the lande also fall to whoredome, and the lande bee full of wickednesse.
“‘Kada ka ƙasƙantar da’yarka ta wurin mai da ita karuwa, in ba haka ba ƙasar za tă juya ga karuwanci tă kuma cika da mugunta.
30 Ye shall keepe my Sabbaths and reuerence my Sanctuarie: I am the Lord.
“‘Ku kiyaye Asabbacina, ku kuma girmama wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji.
31 Ye shall not regarde them that worke with spirites, neither soothsayers: ye shall not seeke to them to be defiled by them: I am the Lord your God.
“‘Kada ku juya ga masu duba, ko ku nemi shawarar bokaye, gama za ku ƙazantu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji Allahnku.
32 Thou shalt rise vp before the horehead, and honour the person of the old man, and dread thy God: I am the Lord.
“‘Ku miƙe tsaye a gaban tsofaffi, ku nuna bangirma ga waɗanda suka tsufa, ku kuma girmama Allahnku. Ni ne Ubangiji.
33 And if a stranger soiourne with thee in your lande, ye shall not vexe him.
“‘Sa’ad da baƙo yana zama tare da ku a ƙasarku, kada ku wulaƙanta shi.
34 But the stranger that dwelleth with you, shalbe as one of your selues, and thou shalt loue him as thy selfe: for ye were strangers in the lad of Egypt: I am the Lord your God.
Dole ku ɗauki baƙon da yake zama tare da ku kamar haifaffe ɗan ƙasa. Ku ƙaunace shi kamar kanku, gama dā ku ma baƙi ne a Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.
35 Ye shall not doe vniustly in iudgement, in line, in weight, or in measure.
“‘Kada ku yi amfani da mudun ƙarya sa’ad da kuke awon tsawo, nauyi, ko yawan abu.
36 You shall haue iust ballances, true weightes, a true Ephah, and a true Hin. I am the Lord your God, which haue brought you out of the lande of Egypt.
Ku yi amfani da ma’auni na gaskiya da mudu na gaskiya, da kuma magwaji na gaskiya. Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar.
37 Therefore shall ye obserue all mine ordinances, and all my iudgements, and doe them: I am the Lord.
“‘Ku kiyaye dukan farillaina da kuma dukan dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.’”

< Leviticus 19 >