< Judges 3 >

1 These nowe are the nations which the Lord left, that he might proue Israel by them (euen as many of Israel as had not knowen all the warres of Canaan,
Waɗannan su ne al’umman da Ubangiji ya bari don yă gwada duk waɗannan Isra’ilawan da ba su san yaƙi a Kan’ana ba
2 Only to make the generations of the children of Israel to know, and to teach them warre, which doutles their predecessors knew not)
(ya yi haka ne domin yă koya wa zuriyar Isra’ilawa waɗanda ba su taɓa yin yaƙi a dā ba),
3 Fiue princes of the Philistims, and all the Canaanites, and the Sidonians, and the Hiuites that dwelt in mount Lebanon, from mount Baal-hermon vntill one come to Hamath.
sarakuna biyar na Filistiyawa, dukan Kan’aniyawa, Sidoniyawa, da kuma Hiwiyawan da suke zaune a duwatsun Lebanon daga Dutsen Ba’al-Hermon zuwa Lebo Hamat.
4 And these remayned to proue Israel by them, to wit, whether they would obey the commandements of the Lord, which he commanded their fathers by the hand of Moses.
An bar su domin su gwada Isra’ilawa a ga ko za su yi biyayya da umarnin Ubangiji, wanda ya ba wa kakanninsu ta wurin Musa.
5 And the children of Israel dwelt among the Canaanites, the Hittites, and the Amorites, and the Perizzites, and the Hiuites, and the Iebusites,
Isra’ilawa suka zauna tare da Kan’aniyawa da Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa.
6 And they tooke their daughters to bee their wiues, and gaue their daughters to their sonnes, and serued their gods.
Suka auri’ya’yansu mata, su ma suka bar’ya’yansu maza suka auri’ya’yansu mata, suka kuma yi wa gumakansu sujada.
7 So the children of Israel did wickedly in the sight of the Lord, and forgate the Lord their God, and serued Baalim, and Asheroth.
Isra’ilawa suka aikata mugunta a gaban Ubangiji; suka manta da Ubangiji Allahnsu suka kuma bauta wa Ba’al da Ashera.
8 Therefore the wrath of the Lord was kindled against Israel, and he solde them into the hand of Chushan rishathaim King of Aram-naharaim, and the children of Israel serued Chushan rishathaim eyght yeeres.
Fushin Ubangiji kuwa ya yi ƙuna a kan Isra’ila har ya sayar da su ga Kushan-Rishatayim sarkin Aram-Naharayim, a wurinsa ne Isra’ilawa suka zama bayi shekara takwas.
9 And when the children of Israel cryed vnto the Lord, the Lord stirred vp a sauiour to ye children of Israel, and he saued them, euen Othniel the sonne of Kenaz, Calebs yonger brother.
Amma da suka yi kuka ga Ubangiji, sai ya tad musu da mai ceto, Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb wanda ya cece su.
10 And the spirite of the Lord came vpon him, and he iudged Israel, and went out to warre: and the Lord deliuered Chushan rishathaim king of Aram into his hand, and his hand preuailed against Chushan rishathaim.
Ruhun Ubangiji ya sauko masa, domin yă zama mahukuncin Isra’ila yă kuma je yaƙi. Ubangiji ya bayar da Kushan-Rishatayim sarkin Aram a hannun Otniyel, ya kuwa sha ƙarfinsa.
11 So the lande had rest fourtie yeeres, and Othniel the sonne of Kenaz dyed.
Saboda haka ƙasar ta zauna da lafiya shekara arba’in har sai da Otniyel ɗan Kenaz ya rasu.
12 Then the children of Israel againe committed wickednesse in the sight of the Lord: and the Lord strengthened Eglon King of Moab against Israel, because they had committed wickednesse before the Lord.
Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda sun aikata wannan mugunta sai Ubangiji ya ba wa Eglon sarkin Mowab ƙarfi a kan Isra’ila.
13 And he gathered vnto him the children of Ammon, and Amalek, and went and smote Israel, and they possessed the citie of palme trees.
Da ya sami Ammonawa da Amalekawa suka haɗa hannu tare, sai Eglon ya tafi ya auka wa Isra’ila, suka ƙwace Birnin Dabino.
14 So the children of Israel serued Eglon king of Moab eighteene yeeres.
Isra’ilawa suka zama bayin Eglon sarkin Mowab shekara goma sha takwas.
15 But when the children of Israel cried vnto the Lord, the Lord stirred them vp a sauiour, Ehud the sonne of Gera the sonne of Iemini, a man lame of his right hande: and the children of Israel sent a present by him vnto Eglon King of Moab.
Isra’ilawa suka sāke yin kuka ga Ubangiji, ya kuwa ba su mai ceto, Ehud, wani bahago, ɗan Gera daga kabilar Benyamin. Isra’ilawa suka aike shi da haraji wurin Eglon sarkin Mowab.
16 And Ehud made him a dagger with two edges of a cubite length, and he did gird it vnder his rayment vpon his right thigh,
To, Ehud ya riga ya ƙera takobi mai kaifi biyu mai tsawo wajen kamu ɗaya da rabi, wanda ya yi ɗamara da shi a cinyarsa ta dama ƙarƙashin rigarsa.
17 And he presented ye gift vnto Eglon King of Moab (and Eglon was a very fat man)
Ya kai wa Eglon sarkin Mowab harajin, wanda yake mai ƙiba ne.
18 And when he had now presented the present, he sent away the people that bare ye present,
Bayan Ehud ya ba da harajin, sai ya sallame mutanen da suka ɗauko harajin.
19 But he turned againe from the quarris, that were by Gilgal, and said, I haue a secret errand vnto thee, O King. Who said, Keepe silence: and all that stoode about him, went out from him.
A wajen gumaka kusa da Gilgal, shi kansa ya juya ya koma ya ce, “Ranka yă daɗe, ina da saƙo na asiri dominka.” Sarkin ya ce, “Ku ba mu wuri!” Sai dukan fadawansa suka fita.
20 Then Ehud came vnto him. (and he sate alone in a sommer parler, which he had) and Ehud said, I haue a message vnto thee from God. Then he arose out of his throne,
Sai Ehud ya matso yayinda shi kuwa yake zaune shi kaɗai a ɗakin sama mai sanyi a fadansa ya ce, “Ina da saƙo daga wurin Allah dominka.” Sarki ya tashi daga kujerarsa,
21 And Ehud put forth his left hand, and tooke the dagger from his right thigh, and thrust it into his bellie,
Ehud ya kai hannun hagunsa, ya zaro takobi daga cinyar ƙafar damansa ya soki sarki a ciki.
22 So that the hafte went in after the blade, and the fatte closed about the blade, so that he could not drawe the dagger out of his bellie, but the dirt came out.
Har ƙotar ma ta shige ciki, takobin kuma ya fito ta bayansa. Ehud bai zare takobin ba, kitse kuwa ya rufe shi.
23 Then Ehud gate him out into the porch, and shut the doores of the parler vpon him, and locked them.
Sa’an nan Ehud ya fita daga shirayin; ya rufe ƙofar ɗakin saman, ya kuma kulle su.
24 And when he was gone out, his seruantes came: who seeing that the doores of the parler were locked, they sayd, Surely he doeth his easement in his sommer chamber.
Bayan da ya tafi, bayin sarki suka zo suka tarar duk ƙofofin ɗakin sama suna kulle, suka ce, “Wataƙila yana bayan gari ne a ɗakin ciki.”
25 And they taryed till they were ashamed: and seeing he opened not the doores of the parler, they tooke the key, and opened them, and behold, their lord was fallen dead on the earth.
Suka yi ta jira har suka gaji. Da suka ga dai bai buɗe ƙofar ba, sai suka ɗauki mabuɗi, suka buɗe. Sai ga shugabansu a ƙasa matacce.
26 So Ehud escaped (while they taried) and was passed the quarris, and escaped vnto Seirah.
Yayinda suke fama jira, Ehud ya riga ya yi gaba. Ya bi ta wajen gumaka zuwa Seyira.
27 And when he came home, he blew a trumpet in mount Ephraim, and the children of Israel went downe with him from the mountaine, and he went before them.
Da ya iso can, sai ya busa ƙaho a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuma suka gangaro tare da shi daga tuddai, shi kuwa yana jagorarsu.
28 Then said he vnto them, Follow me: for the Lord hath deliuered your enemies, euen Moab into your hand. So they went downe after him, and tooke the passages of Iorden towarde Moab, and suffred not a man to passe ouer.
Ya umarce su ya ce, “Ku bi ni, gama Ubangiji ya ba Mowab abokin gābanku a hannunku.” Haka suka gangaro tare da shi suna mallaki mashigin Urdun da ta shiga zuwa Mowab, ba su yarda wani ya haye ba.
29 And they slewe of the Moabites the same time about ten thousand men, all fed men, and all were warriours, and there escaped not a man.
A lokacin sun kashe mutanen Mowab dubu goma, dukansu jarumawa da masu ji da ƙarfi; ba ko ɗaya da ya tsira.
30 So Moab was subdued that daye, vnder the hand of Israel: and the land had rest fourescore yeeres.
A wannan rana aka mai da Mowab bayin Isra’ila, ƙasar kuwa ta sami zaman lafiya shekara takwas.
31 And after him was Shamgar the sonne of Anath, which slewe of the Philistims sixe hundreth men with an oxe goade, and he also deliuered Israel.
Bayan Ehud, sai Shamgar ɗan Anat, wanda ya karkashe Filistiyawa ɗari shida da sandar korar shanun noma, shi ma ya ceci Isra’ila.

< Judges 3 >