< Judges 21 >

1 Moreouer, the men of Israel sware in Mizpeh, saying, None of vs shall giue his daughter vnto the Beniamites to wyfe.
Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
2 And the people came vnto ye house of God and abode there till euen before God, and lift vp their voyces, and wept with great lamentation,
Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
3 And sayde, O Lord God of Israel, why is this come to passe in Israel, that this day one tribe of Israel should want?
Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
4 And on the morow the people rose vp and made there an altar, and offred burnt offrings and peace offrings.
Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
5 Then the children of Israel said, Who is he among all the tribes of Israel, that came not vp with the Congregation vnto the Lord? for they had made a great othe concerning him that came not vp to the Lord to Mizpeh, saying, Let him die the death.
Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
6 And the children of Israel were sory for Beniamin their brother, and said, There is one tribe cut off from Israel this day.
To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
7 How shall we do for wiues to them that remaine, seeing we haue sworne by the Lord, that we will not giue them of our daughters to wiues?
Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
8 Also they saide, Is there any of the tribes of Israel that came not vp to Mizpeh to the Lord? and beholde, there came none of Iabesh Gilead vnto the hoste and to the Congregation.
Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
9 For when the people were vewed; beholde, none of the inhabitants of Iabesh Gilead were there.
Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
10 Therefore the Congregation sent thither twelue thousande men of the most valiant, and commanded them, saying, Goe, and smite the inhabitants of Iabesh Gilead with the edge of the sword, both women, and children.
Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
11 And this is it that ye shall do: ye shall vtterly destroye all the males and all the women that haue lien by men.
Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
12 And they found among the inhabitants of Iabesh Gilead foure hundreth maides, virgins that had knowne no man by lying with any male: and they brought them vnto the hoste to Shiloh, which is in the land of Canaan.
Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
13 Then the whole Congregation sent and spake with the children of Beniamin that were in the rocke of Rimmon, and called peaceably vnto them:
Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
14 And Beniamin came againe at that time, and they gaue them wiues which they had saued aliue of the women of Iabesh Gilead: but they had not so ynough for them.
Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
15 And the people were sorie for Beniamin, because the Lord had made a breach in the tribes of Israel.
Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
16 Therefore the Elders of the Congregation said, How shall we doe for wiues to the remnant? for the women of Beniamin are destroyed.
Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
17 And they saide, there must be an inheritance for them that be escaped of Beniamin, that a tribe be not destroyed out of Israel.
Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
18 Howbeit we may not giue them wiues of our daughters: for the childre of Israel had sworne, saying, Cursed be he that giueth a wise to Beniamin.
Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
19 Therefore they said, Beholde, there is a feast of the Lord euery yere in Shiloh in a place, which is on the Northside of Beth-el, and on the Eastside of the way that goeth vp from Beth-el to Shechem, and on the South of Lebonah.
Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
20 Therefore they commanded the children of Beniamin, saying, Goe, and lye in waite in the vineyardes.
Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
21 And when ye see that the daughters of Shiloh come out to dance in dances, then come ye out of the vineyards, and catche you euery man a wife of the daughters of Shiloh, and goe into the land of Beniamin.
ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
22 And when their fathers or their brethren come vnto vs to complaine, we wil say vnto them, Haue pitie on them for our sakes, because we reserued not to eche man his wife in the warre, and because ye haue not giuen vnto them hitherto, ye haue sinned.
Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
23 And the children of Beniamin did so, and tooke wiues of them that danced according to their nomber: which they tooke, and went away, and returned to their inheritance, and repaired the cities and dwelt in them.
Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
24 So the children of Israel departed thence at that time, euery man to his tribe, and to his familie, and went out from thence euery man to his inheritance.
A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
25 In those dayes there was no King in Israel, but euery man did that which was good in his eyes.
A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.

< Judges 21 >