< Job 34 >

1 Moreouer Elihu answered, and saide,
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 Heare my wordes, ye wise men, and hearken vnto me, ye that haue knowledge.
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 For the eare tryeth the words, as the mouth tasteth meate.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Let vs seeke iudgement among vs, and let vs knowe among our selues what is good.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 For Iob hath saide, I am righteous, and God hath taken away my iudgement.
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 Should I lye in my right? my wound of the arrowe is grieuous without my sinne.
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 What man is like Iob, that drinketh scornfulnesse like water?
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 Which goeth in the companie of them that worke iniquitie, and walketh with wicked men?
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 For he hath saide, It profiteth a man nothing that he should walke with God.
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 Therefore hearken vnto me, ye men of wisedome, God forbid that wickednesse should be in God, and iniquitie in the Almightie.
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 For he will render vnto man according to his worke, and cause euery one to finde according to his way.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 And certainely God will not do wickedly, neither will the Almightie peruert iudgement.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Whome hath he appointed ouer the earth beside him selfe? or who hath placed the whole worlde?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 If he set his heart vpon man, and gather vnto him selfe his spirit and his breath,
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 All flesh shall perish together, and man shall returne vnto dust.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 And if thou hast vnderstanding, heare this and hearken to the voyce of my wordes.
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Shal he that hateth iudgement, gouerne? and wilt thou iudge him wicked that is most iust?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Wilt thou say vnto a King, Thou art wicked? or to princes, Ye are vngodly?
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 How much lesse to him that accepteth not the persons of princes, and regardeth not the rich, more then the poore? for they be all the worke of his handes.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 They shall die suddenly, and the people shalbe troubled at midnight, and they shall passe foorth and take away the mightie without hand.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 For his eyes are vpon the wayes of man, and he seeth all his goings.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 There is no darkenesse nor shadowe of death, that the workers of iniquitie might be hid therein.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 For he will not lay on man so much, that he should enter into iudgement with God.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 He shall breake the mightie without seeking, and shall set vp other in their stead.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 Therefore shall he declare their works: he shall turne the night, and they shalbe destroyed.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 He striketh them as wicked men in the places of the seers,
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 Because they haue turned backe from him, and would not consider all his wayes:
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 So that they haue caused the voyce of the poore to come vnto him, and he hath heard the cry of the afflicted.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 And when he giueth quietnesse, who can make trouble? and when he hideth his face, who can beholde him, whether it be vpon nations, or vpon a man onely?
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 Because the hypocrite doeth reigne, and because the people are snared.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 Surely it appertaineth vnto God to say, I haue pardoned, I will not destroy.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 But if I see not, teach thou me: if I haue done wickedly, I will doe no more.
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Wil he performe the thing through thee? for thou hast reproued it, because that thou hast chosen, and not I. now speake what thou knowest.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Let men of vnderstanding tell me, and let a wise man hearken vnto me.
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 Iob hath not spoken of knowledge, neyther were his wordes according to wisedome.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 I desire that Iob may be tryed, vnto the ende touching the answeres for wicked men.
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 For he addeth rebellion vnto his sinne: he clappeth his handes among vs, and multiplieth his wordes against God.
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >