< Job 31 >

1 I made a couenant with mine eyes: why then should I thinke on a mayde?
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 For what portion should I haue of God from aboue? and what inheritance of the Almightie from on hie?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 Is not destruction to the wicked and strange punishment to the workers of iniquitie?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 Doeth not he beholde my wayes and tell all my steps?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 If I haue walked in vanitie, or if my foote hath made haste to deceite,
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 Let God weigh me in the iust balance, and he shall know mine vprightnes.
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 If my steppe hath turned out of the way, or mine heart hath walked after mine eye, or if any blot hath cleaued to mine handes,
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 Let me sowe, and let another eate: yea, let my plantes be rooted out.
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 If mine heart hath bene deceiued by a woman, or if I haue layde wayte at the doore of my neighbour,
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 Let my wife grinde vnto another man, and let other men bow downe vpon her:
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 For this is a wickednes, and iniquitie to bee condemned:
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 Yea, this is a fire that shall deuoure to destruction, and which shall roote out al mine increase,
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 If I did contemne the iudgement of my seruant, and of my mayde, when they did contend with me,
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 What then shall I do when God standeth vp? and when he shall visit me, what shall I answere?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 He that hath made me in the wombe, hath he not made him? hath not he alone facioned vs in the wombe?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 If I restrained the poore of their desire, or haue caused the eyes of the widow to faile,
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 Or haue eaten my morsels alone, and the fatherles hath not eaten thereof,
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 (For from my youth hee hath growen vp with me as with a father, and from my mothers wombe I haue bene a guide vnto her)
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 If I haue seene any perish for want of clothing, or any poore without couering,
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 If his loynes haue not blessed me, because he was warmed with the fleece of my sheepe,
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 If I haue lift vp mine hande against the fatherlesse, when I saw that I might helpe him in the gate,
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 Let mine arme fal from my shoulder, and mine arme be broken from the bone.
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 For Gods punishment was fearefull vnto me, and I could not be deliuered from his highnes.
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 If I made gold mine hope, or haue sayd to the wedge of golde, Thou art my confidence,
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 If I reioyced because my substance was great, or because mine hand had gotten much,
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 If I did behold the sunne, when it shined, or the moone, walking in her brightnes,
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 If mine heart did flatter me in secrete, or if my mouth did kisse mine hand,
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 (This also had bene an iniquitie to be condemned: for I had denied the God aboue)
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 If I reioyced at his destruction that hated me, or was mooued to ioye when euill came vpon him,
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 Neither haue I suffred my mouth to sinne, by wishing a curse vnto his soule.
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 Did not the men of my Tabernacle say, Who shall giue vs of his flesh? we can not bee satisfied.
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 The stranger did not lodge in the streete, but I opened my doores vnto him, that went by the way.
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 If I haue hid my sinne, as Adam, concealing mine iniquitie in my bosome,
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 Though I could haue made afraid a great multitude, yet the most contemptible of the families did feare me: so I kept silence, and went not out of the doore.
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 Oh that I had some to heare me! beholde my signe that the Almightie will witnesse for me: though mine aduersary should write a booke against me,
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 Woulde not I take it vpon my shoulder, and binde it as a crowne vnto me?
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 I will tell him the nomber of my goings, and goe vnto him as to a prince.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 If my lande cry against me, or the furrowes thereof complayne together,
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 If I haue eaten the fruites thereof without siluer: or if I haue grieued the soules of the masters thereof,
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 Let thistles growe in steade of wheate, and cockle in the stead of Barley. The wordes of Iob are ended.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.

< Job 31 >