< Job 2 >

1 And on a day the children of God came and stood before the Lord, and Satan came also among them, and stoode before the Lord.
Wata rana kuma mala’iku suka sāke kawo kansu gaban Ubangiji, sai Shaiɗan shi ma ya zo tare da su yă nuna kansa a gabansa.
2 Then the Lord sayde vnto Satan, Whence commest thou? And Satan answered the Lord, and sayd, From compassing the earth to and from, and from walking in it.
Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
3 And the Lord sayd vnto Satan, Hast thou not considered my seruant Iob, how none is like him in the earth? an vpright and iust man, one that feareth God, and escheweth euill? for yet he continueth in his vprightnesse, although thou mouedst me against him, to destroy him without cause.
Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah ba ruwansa da mugunta. Kuma har yanzu bai fasa zama mai aminci ba duk da wahalar da ka sa na bari ka ba shi ba tare da wani dalili ba.”
4 And Satan answered the Lord, and sayde, Skin for skin, and all that euer a man hath, will he giue for his life.
Shaiɗan ya amsa ya ce, “Fata don fata! Mutum zai iya rabuwa da duk abin da yake da shi domin ransa.
5 But stretch now out thine hand, and touch his bones and his flesh, to see if he will not blaspheme thee to thy face.
Ka ɗan taɓa lafiyar jikinsa ka gani ba shakka zai la’anta ka kana ji kana gani.”
6 Then the Lord said vnto Satan, Lo, he is in thine hand, but saue his life.
Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.”
7 So Satan departed from the presence of the Lord, and smote Iob with sore boyles, from the sole of his foote vnto his crowne.
Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji, ya je ya sa wa Ayuba ƙuraje masu zafi a jikinsa daga tafin ƙafafunsa har zuwa kansa.
8 And he tooke a potsharde to scrape him, and he sate downe among the ashes.
Sai Ayuba ya ɗauki kaskon tukunya yana ta sosa ƙurajen da shi, yayinda yake zaune cikin toka.
9 Then said his wife vnto him, Doest thou continue yet in thine vprightnes? Blaspheme God, and dye.
Matarsa ta ce masa, “Har yanzu kana nan da amincinka? Ka la’anta Allah ka mutu!”
10 But he said vnto her, Thou speakest like a foolish woman: what? shall we receiue good at the hande of God, and not receiue euill? In all this did not Iob sinne with his lippes.
Ya amsa ya ce, “Kina magana kamar wawiya. Alheri kaɗai za mu dinga samu daga Allah ban da wahala?” A cikin wannan duka Ayuba bai yi zunubi ba cikin maganarsa.
11 Nowe when Iobs three friends heard of all this euill that was come vpon him, they came euery one from his owne place, to wit, Eliphaz the Temanite, and Bildad the Shuhite, and Zophar the Naamathite: for they were agreed together to come to lament with him, and to comfort him.
Lokacin da abokan Ayuba su uku wato, Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa, da Zofar mutumin Na’ama suka ji wahalar da ta auka wa Ayuba, sai suka shirya suka bar gidajensu suka je don su ta’azantar da shi.
12 So when they lift vp their eyes a farre off, they knewe him not: therefore they lift vp their voyces and wept, and euery one of them rent his garment, and sprinkled dust vpon their heads toward the heauen.
Sa’ad da suka gan shi daga nesa, da ƙyar suka gane shi; sai suka fara kuka da ƙarfi, suka yayyaga tufafinsu suka zuba toka a kawunansu,
13 So they sate by him vpon the ground seuen dayes, and seuen nights, and none spake a worde vnto him: for they sawe, that the griefe was very great.
sai suka zauna da shi a ƙasa har kwana bakwai. Ba wanda ya ce masa kome, don sun ga tsananin wahalar da yake ciki.

< Job 2 >