< Job 14 >

1 Man that is borne of woman, is of short continuance, and full of trouble.
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2 He shooteth foorth as a flowre, and is cut downe: he vanisheth also as a shadowe, and continueth not.
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3 And yet thou openest thine eyes vpon such one, and causest me to enter into iudgement with thee.
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4 Who can bring a cleane thing out of filthinesse? there is not one.
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5 Are not his dayes determined? the nober of his moneths are with thee: thou hast appointed his boundes, which he can not passe.
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6 Turne from him that he may cease vntill his desired day, as an hyreling.
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
7 For there is hope of a tree, if it bee cut downe, that it will yet sproute, and the branches thereof will not cease.
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
8 Though the roote of it waxe olde in the earth, and the stocke thereof be dead in ye ground,
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
9 Yet by the sent of water it will bud, and bring foorth boughes like a plant.
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
10 But man is sicke, and dyeth, and man perisheth, and where is he?
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
11 As the waters passe from the sea, and as the flood decayeth and dryeth vp,
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
12 So man sleepeth and riseth not: for hee shall not wake againe, nor be raised from his sleepe till the heauen be no more.
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
13 Oh that thou wouldest hide me in the graue, and keepe me secret, vntill thy wrath were past, and wouldest giue me terme, and remember me. (Sheol h7585)
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
14 If a man die, shall he liue againe? All the dayes of mine appointed time will I waite, till my changing shall come.
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
15 Thou shalt call me, and I shall answere thee: thou louest the worke of thine own hands.
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
16 But nowe thou nombrest my steppes, and doest not delay my sinnes.
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
17 Mine iniquitie is sealed vp, as in a bagge, and thou addest vnto my wickednesse.
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
18 And surely as the mountaine that falleth, commeth to nought, and the rocke that is remooued from his place:
“Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
19 As the water breaketh the stones, when thou ouerflowest the things which growe in the dust of ye earth: so thou destroyest ye hope of man.
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
20 Thou preuailest alway against him, so that he passeth away: he changeth his face when thou castest him away.
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
21 And he knoweth not if his sonnes shall be honourable, neither shall he vnderstand concerning them, whether they shalbe of lowe degree,
Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
22 But while his flesh is vpon him, he shall be sorowfull, and while his soule is in him, it shall mourne.
Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”

< Job 14 >