< Job 1 >

1 There was a man in the lande of Vz called Iob, and this man was an vpright and iust man, one that feared God, and eschewed euill.
A ƙasar Uz akwai wani mutum mai suna Ayuba. Mutum ne marar laifi kuma mai adalci; yana tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.
2 And he had seue sonnes, and three daughters.
Yana da’ya’ya maza bakwai da’yan mata uku,
3 His substance also was seuen thousande sheepe, and three thousand camels, and fiue hundreth yoke of oxen, and fiue hundreth shee asses, and his family was very great, so that this man was the greatest of all the men of the East.
yana da tumaki dubu bakwai, raƙuma dubu uku, shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, yana kuma da masu yi masa aiki da yawa. A ƙasar Gabas ba wani kamar sa.
4 And his sonnes went and banketted in their houses, euery one his day, and sent, and called their three sisters to eate and to drinke with them.
’Ya’yansa maza sukan yi biki a gidajensu, wannan yă yi yă ba wancan, sai su kira’yan’uwansu mata ukun su ci, su sha tare.
5 And when the dayes of their banketting were gone about, Iob sent, and sanctified them, and rose vp early in the morning, and offred burnt offrings according to the nomber of them all. For Iob thought, It may be that my sonnes haue sinned, and blasphemed God in their hearts: thus did Iob euery day.
Bayan lokacin bikin ya wuce, sai Ayuba yă aika su zo don yă tsarkake su. Tun da sassafe zai miƙa hadaya ta ƙonawa domin kowannensu, don yana tunani cewa, “Mai yiwuwa’ya’yana sun yi wa Allah zunubi, ko sun la’anta shi a cikin zuciyarsu.” Haka Ayuba ya saba yi.
6 Nowe on a day when the children of God came and stoode before the Lord, Satan came also among them.
Wata rana mala’iku suka kawo kansu gaban Ubangiji, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su.
7 Then the Lord sayde vnto Satan, Whence commest thou? And Satan answered the Lord, saying, From compassing the earth to and from, and from walking in it.
Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
8 And the Lord saide vnto Satan, Hast thou not considered my seruant Iob, how none is like him in the earth? an vpright and iust man, one that feareth God, and escheweth euill?
Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.”
9 Then Satan answered the Lord, and sayde, Doeth Iob feare God for nought?
Sai Shaiɗan ya amsa ya ce, “Haka kawai Ayuba yake tsoron Allah?
10 Hast thou not made an hedge about him and about his house, and about all that he hath on euery side? thou hast blessed the worke of his hands, and his substance is increased in the land.
Ba ka kāre shi da iyalinsa gaba ɗaya da duk mallakarsa ba? Ka Albarkaci ayyukan hannunsa yadda dabbobinsa duk sun cika ko’ina.
11 But stretch out now thine hand and touch all that he hath, to see if he will not blaspheme thee to thy face.
Ka ɗan miƙa hannunka ka raba shi da duk abin da yake da shi, ba shakka zai la’anta ka kana ji, kana gani.”
12 Then the Lord sayde vnto Satan, Lo, all that he hath is in thine hand: onely vpon himselfe shalt thou not stretch out thine hand. So Satan departed from the presence of the Lord.
Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.” Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji.
13 And on a day, when his sonnes and his daughters were eating and drinking wine in their eldest brothers house,
Wata rana lokacin da’ya’yan Ayuba suke cikin biki a gidan babban ɗansa,
14 There came a messenger vnto Iob, and said, The oxen were plowing, and the asses feeding in their places,
sai ɗan aika ya zo wurin Ayuba ya ce masa, “Shanu suna huɗa, jakuna kuma suna kiwo nan kusa,
15 And the Shabeans came violently, and tooke them: yea, they haue slayne the seruants with the edge of the sworde: but I onely am escaped alone to tell thee.
sai Sabenawa suka auka musu suka kwashe su suka tafi, suka karkashe masu yi maka aiki duka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
16 And whiles he was yet speaking, another came, and sayde, The fire of God is fallen from the heauen, and hath burnt vp the sheepe and the seruants, and deuoured them: but I onely am escaped alone to tell thee.
Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Wutar Allah ta sauko daga sama ta ƙona dukan tumaki da masu lura da su, wato, bayinka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
17 And whiles he was yet speaking, another came, and sayd, The Caldeans set on three bands, and fell vpon the camels, and haue taken them, and haue slayne the seruantes with the edge of the sworde: but I onely am escaped alone to tell thee.
Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa sun auka wa raƙumanka sun kwashe su duka, suka kuma karkashe masu yi maka aiki, ni kaɗai ne na tsira na zo in gaya maka!”
18 And whiles he was yet speaking, came an other, and sayd, Thy sonnes, and thy daughters were eating, and drinking wine in their eldest brothers house,
Yana cikin magana, sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “’Ya’yanka maza da mata suna biki, suna ci suna sha a gidan babban ɗanka,
19 And behold, there came a great wind from beyonde the wildernesse, and smote the foure corners of the house, which fel vpon the children, and they are dead, and I onely am escaped alone to tell thee.
sai wata iska mai ƙarfi daga hamada ta auka ta rushe gidan, gidan kuwa ya fāɗi a kan’ya’yanka ya kashe su, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
20 Then Iob arose, and rent his garment, and shaued his head, and fel downe vpon the ground, and worshipped,
Da jin haka sai Ayuba ya tashi ya yayyaga tufafin jikinsa, ya aske kansa. Ya fāɗi a ƙasa ya yi sujada
21 And sayd, Naked came I out of my mothers wombe, and naked shall I returne thither: the Lord hath giuen, and the Lord hath taken it: blessed be the Name of the Lord.
ya ce, “Tsirara na fito daga cikin mahaifiyata, tsirara kuma zan koma. Ubangiji ya bayar, Ubangiji kuma ya karɓa; yabo ya tabbata ga Ubangiji.”
22 In all this did not Iob sinne, nor charge God foolishly.
Cikin wannan duka Ayuba bai yi wa Allah zunubi ta wurin ba shi laifi ba.

< Job 1 >