< Jeremiah 50 >

1 The word that the Lord spake, concerning Babel, and cocerning the land of the Caldeans by the ministerie of Ieremiah the Prophet.
Ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Irmiya annabi game da Babilon da kuma ƙasar Babiloniyawa.
2 Declare among the nations, and publish it, and set vp a standart, proclaime it and conceale it not: say, Babel is taken, Bel is confounded, Merodach is broken downe: her idols are confounded, and their images are burst in pieces.
“Ka yi shela ka kuma furta a cikin al’ummai, ka tā da tuta ka kuma furta; kada ku ɓoye kome, amma ku ce, ‘Za a ci Babilon da yaƙi; za a kunyata Bel, Marduk ya cika da tsoro. Siffofinta za su sha kunya gumakanta za su cika da tsoro.’
3 For out of the North there commeth vp a nation against her, which shall make her lande waste, and none shall dwel therein: they shall flee, and depart, both man and beast.
Al’umma daga arewa za tă fāɗa mata su mai da ƙasar kango. Ba wanda zai zauna a cikinta; mutane da dabbobi za su gudu.
4 In those daies, and at that time, sayeth the Lord, the children of Israel shall come, they, and the children of Iudah together, going, and weeping shall they goe, and seeke the Lord their God.
“A kwanakin nan, a wannan lokaci,” in ji Ubangiji, “mutanen Isra’ila da mutanen Yahuda gaba ɗaya za su tafi cikin hawaye su nemi Ubangiji Allahnsu.
5 They shall aske the way to Zion, with their faces thitherward, saying, Come, and let vs cleaue to the Lord in a perpetuall couenant that shall not be forgotten.
Za su tambayi hanyar zuwa Sihiyona su kuma juya fuskokinsu wajenta. Za su zo su haɗa kansu ga Ubangiji a madawwamin alkawari da ba za a manta da shi ba.
6 My people hath beene as lost sheepe: their shepheards haue caused them to goe astray, and haue turned them away to the mountaines: they haue gone from mountaine to hil, and forgotten their resting place.
“Mutanena sun zama ɓatattun tumaki; makiyayansu sun bauɗar da su suka sa suna ta yawo a cikin duwatsu. Sun yi ta yawo a bisa dutse da tudu suka manta wurin hutunsu.
7 Al that found them, haue deuoured them, and their enemies saide, We offende not, because they haue sinned against the Lord, the habitation of iustice, euen the Lord the hope of their fathers.
Duk wanda ya same su ya cinye su; abokan gābansu suka ce, ‘Ba mu da laifi, gama sun yi zunubi wa Ubangiji, wurin kiwonsu na gaske, Ubangiji, abin sa zuciyar kakanninsu.’
8 Flee from the middes of Babel, and depart out of the lande of the Caldeans, and be ye as the hee goates before the flocke.
“Ku gudu daga Babilon; ku bar ƙasar Babiloniyawa, ku zama kamar awakin da suke bi da garke.
9 For loe, I will raise, and cause to come vp against Babel a multitude of mightie natios from the North countrey, and they shall set themselues in aray against her, whereby shee shall be taken: their arrowes shall be as of a strong man, which is expert, for none shall returne in vaine.
Gama zan kuta in kuma kawo a kan Babilon haɗinkan manyan al’ummai na arewa. Za su ja dāgār gāba da ita, kuma daga arewa za a ci ta da yaƙi. Kibiyoyinsu za su zama kamar na gwanayen jarumawa waɗanda ba sa dawowa hannu wofi.
10 And Caldea shalbe a spoyle: all that spoyle her, shalbe satisfied, sayth the Lord.
Saboda haka za a washe Babiloniyawa; dukan waɗanda suka washe ta za su ƙoshi,” in ji Ubangiji.
11 Because yee were glad and reioyced in destroying mine heritage, and because ye are growen fatte, as the calues in the grasse, and neied like strong horses,
“Saboda kuna farin ciki kuna kuma murna, ku da kuka washe gādona, domin kuna tsalle kamar karsana mai sussuka hatsi kuna kuma haniniya kamar ingarmu.
12 Therefore your mother shall bee sore confounded, and she that bare you, shall be ashamed: beholde, the vttermost of the nations shalbe a desert, a drie land, and a wildernes.
Mahaifiyarku za tă sha babbar kunya; ita da ta haife ku za tă sha kunya. Za tă zama mafi ƙanƙanta na al’ummai, jeji, busasshiyar ƙasa, hamada.
13 Because of the wrath of the Lord it shall not be inhabited, but shall be wholy desolate: euery one that goeth by Babel, shall be astonished, and hisse at all her plagues.
Saboda fushin Ubangiji ba za tă zauna a cikinta ba amma za tă zama kufai gaba ɗaya. Duk waɗanda suka wuce Babilon za su ji tsoro su kuma yi tsaki saboda dukan mikinta.
14 Put your selues in aray against Babel rounde about: all ye that bende the bowe, shoote at her, spare no arrowes: for shee hath sinned against the Lord.
“Ku ja dāgā kewaye da Babilon, dukanku waɗanda kuke jan baka. Ku harbe ta! Kada ku rage kibiyoyi, gama ta yi zunubi ga Ubangiji.
15 Crie against her round about: she hath giuen her hand: her foundations are fallen, and her walles are destroyed: for it is the vengeance of the Lord: take vengeance vpon her: as she hath done, doe vnto her.
Ku yi kuwwa a kanta a kowane gefe! Ta miƙa wuya, hasumiyarta ta fāɗi, katangarta sun rushe. Da yake wannan sakayya ce ta Ubangiji, ku ɗauki fansa a kanta; yi mata yadda ta yi wa waɗansu.
16 Destroy the sower from Babel, and him that handleth the sieth in the time of haruest: because of the sworde of the oppressor they shall turne euery one to his people, and they shall flee euery one to his owne land.
Ku datse wa Babilon mai shuka, da mai girbi lauje a lokacin girbi. Saboda takobin mai zalunci bari kowa ya koma ga mutanensa, bari kowa ya gudu zuwa ga ƙasarsa.
17 Israel is like scattered sheepe: the lions haue dispersed them: first the King of Asshur hath deuoured him, and last this Nebuchad-nezzar King, of Babel hath broken his bones.
“Isra’ila garke ne da ya watse da zakoki suka kora. Na farkon da ya cinye shi sarkin Assuriya ne; na ƙarshen da ya ragargaza ƙasusuwansa Nebukadnezzar sarkin Babilon ne.”
18 Therefore thus saith the Lord of hostes the God of Israel, Behold, I wil visit ye King of Babel, and his land, as I haue visited the King of Asshur.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Zan hukunta sarkin Babilon da ƙasarsa yadda na hukunta sarkin Assuriya.
19 And I will bring Israel againe to his habitation: hee shall feede on Carmel and Bashan, and his soule shall be satisfied vpon the mount Ephraim and Gilead.
Amma zan komo da Isra’ila zuwa wurin kiwonsa zai kuwa yi kiwo a Karmel da Bashan; zai ƙosar da marmarinsa a tuddan Efraim da Gileyad.
20 In those daies, and at that time, sayeth the Lord, the iniquitie of Israel shall be sought for, and there shall be none: and the sinnes of Iudah, and they shall not be founde: for I will be mercifull vnto them, whome I reserue.
A kwanakin nan, da kuma a lokacin nan,” in ji Ubangiji, “za a yi bincike don laifin Isra’ila, amma ba za a samu ba, kuma don zunubin Yahuda, amma ba za a sami wani abu ba, gama zan gafarta wa raguwar da na rage.
21 Goe vp against the lande of the rebelles, euen against it, and against the inhabitantes of Pekod: destroy, and lay it waste after them, saieth the Lord, and doe according to all that I haue commanded thee.
“Ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da waɗanda suke zama a Fekod. Ku fafara, ku kashe kuma hallaka su sarai,” in ji Ubangiji. “Ku aikata dukan abin da na umarce ku.
22 A crie of battell is in the land, and of great destruction.
Hargowar yaƙi tana a ƙasar, hargowar babbar hallaka!
23 Howe is the hammer of the whole world destroied, and broken! howe is Babel become desolate among the nations!
Dubi yadda aka karya aka kuma ragargaza gudumar dukan duniya! Dubi yadda Babilon ta zama kufai a cikin al’ummai!
24 I haue snared thee, and thou art taken, O Babel, and thou wast not aware: thou art found, and also caught, because thou hast striuen against the Lord.
Na sa miki tarko, Babilon, kika kuwa kamu kafin ki sani; aka same ki aka kuma kama ki domin kin tayar wa Ubangiji.
25 The Lord hath opened his treasure, and hath brought foorth the weapons of his wrath: for this is the woorke of the Lord God of hostes in the lande of the Caldeans.
Ubangiji ya buɗe taskar makamansa ya fitar da makaman fushinsa, gama Maɗaukaki Ubangiji Mai Iko Duka yana da aikin da zai yi a ƙasar Babiloniyawa.
26 Come against her from the vtmost border: open her store houses: treade on her as on sheaues, and destroy her vtterly: let nothing of her be left.
Ku zo ku yi gāba da ita daga nesa. Ku buɗe rumbunanta; ku jibga ta kamar tsibin hatsi. Ku hallaka ta sarai kada ku bar mata raguwa.
27 Destroy all her bullockes: let them goe downe to the slaughter. Wo vnto them, for their day is come, and the time of their visitation.
Ku kashe dukan’yan bijimanta bari su gangara zuwa mayanka! Kaitonsu! Gama ranansu ta zo, lokaci ya yi da za a hukunta su.
28 The voyce of them that flee, and escape out of the lande of Babel to declare in Zion the vengeance of the Lord our God, and the vengeance of his Temple.
Ku saurari masu gudun hijira da masu neman mafaka daga Babilon suna furtawa a Sihiyona yadda Ubangiji Allahnmu ya ɗauki fansa, fansa domin haikalinsa.
29 Call vp the archers against Babel: al ye that bend the bow, besiege it rounde about: let none thereof escape: recompence her according to her worke, and according to all that she hath done, doe vnto her: for she hath bene proud against the Lord, euen against the holy one of Israel.
“Ku kira’yan baka a kan Babilon, dukan waɗanda suke jan baka. Ku yi sansani kewaye da ita duka; kada ku bar wani ya tsira. Ku sāka mata don ayyukanta; ku yi mata yadda ta yi. Gama ta tayar wa Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
30 Therefore shall her yong men fall in the streetes, and al her men of warre shalbe destroied in that day, sayeth the Lord.
Saboda haka, samarinta za su fāɗi a tituna; za a kawar da dukan sojojinta a wannan rana,” in ji Ubangiji.
31 Beholde, I come vnto thee, O proude man, saith the Lord God of hostes: for thy day is come, euen the time that I will visite thee.
“Ga shi, ina gāba da ke, ya ke mai girman kai,” in ji Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, “gama ranarki ta zo, lokacin da za a hukunta ki.
32 And the proude shall stumble and fall, and none shall raise him vp: and I will kindle a fire in his cities, and it shall deuoure all round about him.
Mai ɗaga kai za tă yi tuntuɓe ta kuma fāɗi kuma ba wanda zai taimake ta tă tashi; zan hura wuta a garuruwanta da za tă cinye duk waɗanda suke kewaye da ita.”
33 Thus saieth the Lord of hosts, The children of Israel, and the children of Iudah were oppressed together: and all that tooke them captiues, held them, and would not let them goe.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “An danne mutanen Isra’ila, haka ma mutanen Yahuda. Dukan waɗanda suka kama su suna riƙe su kankan, suna kin barinsu su tafi.
34 But their strong redeemer, whose Name is the Lord of hostes, he shall maintaine their cause, that he may giue rest to the lande, and disquiet the inhabitants of Babel.
Duk da haka Mai Fansarsu yana da ƙarfi; Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa. Zai kāre muradunsu gabagadi don yă kawo hutu ga ƙasarsu, amma rashin hutu ga waɗanda suke zaune a Babilon.
35 A sworde is vpon the Caldeans, sayeth the Lord, and vpon the inhabitants of Babel, and vpon her princes, and vpon her wise men.
“Akwai takobi a kan Babiloniyawa!” In ji Ubangiji “a kan waɗanda suke zama a Babilon da kuma a kan fadawanta da masu hikimarta!
36 A sworde is vpon the soothsaiers, and they shall dote: a sword is vpon her strong men, and they shalbe afraide.
Akwai takobi a kan annabawan ƙaryanta! Za su zama wawaye. Akwai takobi a kan jarumawanta! Za su cika da tsoro.
37 A sworde is vpon their horses and vpon their charets, and vpon all the multitude that are in the middes of her, and they shall be like women: a sworde is vpon her treasures, and they shall be spoyled.
Akwai takobi a kan dawakanta da kekunan yaƙinta da kuma dukan baƙin da suke cikin mayaƙanta! Za su zama mata. Akwai takobi a kan dukiyarta! Za a washe su.
38 A drought is vpon her waters, and they shall be dried vp: for it is the lande of grauen images, and they dote vpon their idoles.
Fări a kan ruwanta! Za su bushe ƙaf. Gama ƙasa ce ta gumaka, gumakan da za su haukace da tsoro.
39 Therefore the Ziims with the Iims shall dwel there, and the ostriches shall dwel therein: for it shall be no more inhabited, neither shall it be inhabited from generation vnto generation.
“Saboda haka halittun hamada da kuraye za su zauna a can, a can kuma mujiya za tă zauna. Ba za a ƙara zauna ko a yi zama a cikinta ba daga tsara zuwa tsara.
40 As God destroied Sodom and Gomorah with the places thereof neere about, sayeth the Lord: so shall no man dwell theere, neither shall the sonne of man remaine therein.
Yadda Allah ya tumɓuke Sodom da Gomorra tare da maƙwabtan garuruwansu,” in ji Ubangiji “haka ma ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
41 Beholde, a people shall come from the North, and a great nation, and many Kings shall be raised vp from the coastes of the earth.
“Duba! Ga sojoji suna zuwa daga arewa; babbar al’umma da sarakuna masu yawa suna tahowa daga iyakokin duniya.
42 They shall holde the bowe and the buckeler: they are cruell and vnmercifull: their voyce shall roare like the sea, and they shall ride vpon horses, and be put in aray like men to the battell against thee, O daughter of Babel.
Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne marasa tausayi. Amonsu ya yi kamar rurin teku yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa kamar mutane a dāgār yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Babilon.
43 The King of Babel hath heard the report of them, and his hands waxed feeble: sorow came vpon him, euen sorowe as of a woman in trauaile.
Sarkin Babilon ya ji rahotanni game da su, hannunsa kuma ya yi laƙwas. Wahala ta kama shi, zafi kamar na mace mai naƙuda.
44 Beholde, hee shall come vp like a lyon from the swelling of Iorden vnto the strong habitation: for I will make Israel to rest, and I will make them to haste away from her: and who is a chosen man that I may appoynt against her? for who is like me, and who will appoynt me the time? and who is the shepheard that will stande before me?
Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai dausayi, zan fafare Babilon daga ƙasan nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa domin wannan? Wane ne kamar ni da zai kalubalance ni? Kuma wanda makiyayi zai iya tsaya gāba da ni?”
45 Therefore heare the counsell of the Lord that hee hath deuised against Babel, and his purpose that hee hath conceiued against the lande of the Caldeans: surely the least of the flocke shall drawe them out: surely he shall make their habitation desolate with them.
Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Babilon, abin da ya nufa gāba da ƙasar Babiloniyawa. Za a kwashe ƙananan garkensu a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
46 At the noyse of the winning of Babel the earth is moued, and the crye is heard among the nations.
Da jin an ci Babilon da yaƙi sai duniya ta girgiza; za a ji kukanta cikin al’ummai.

< Jeremiah 50 >