< Jeremiah 37 >

1 And King Zedekiah the sonne of Iosiah reigned for Coniah the sonne of Iehoiakim, whome Nebuchad-nezzar King of Babel made King in the land of Iudah.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya naɗa Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda; ya yi mulki a madadin Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim.
2 But neither he, nor his seruants, nor the people of the land would obey the wordes of the Lord, which he spake by the ministerie of the Prophet Ieremiah.
Shi da masu yin masa hidima da mutanen ƙasar ba su kula da maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya annabi ba.
3 And Zedekiah the King sent Iehucal the sonne of Shelemiah, and Zephaniah the sonne of Maaseiah the Priest to the Prophet Ieremiah, saying, Pray now vnto the Lord our God for vs.
Sai sarki Zedekiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya tare da firist nan Zefaniya ɗan Ma’asehiya da wannan saƙo cewa, “Ina roƙonka ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnmu saboda mu.”
4 (Now Ieremiah went in and out among the people: for they had not put him into the prison.
To, fa, Irmiya ya sami’yancin kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a riga an sa shi a kurkuku ba.
5 Then Pharaohs hoste was come out of Egypt: and when the Caldeans that besieged Ierusalem, heard tidings of them, they departed from Ierusalem)
Sojojin Fir’auna suka fita daga Masar, sa’ad da Babiloniyawa waɗanda suke ƙawanya wa Urushalima suka ji labari game da su, sai suka janye daga Urushalima.
6 Then came the worde of the Lord vnto the Prophet Ieremiah, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya annabi cewa,
7 Thus sayth the Lord God of Israel, Thus shall ye say to the King of Iudah, that sent you vnto me to inquire of me, Behold, Pharaohs hoste, which is come forth to helpe you, shall returne to Egypt into their owne land.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
8 And the Caldeans shall come againe, and fight against this citie, and take it and burne it with fire.
Sa’an nan Babiloniyawa za su koma su yaƙi wannan birni su ci ta su kuma ƙone shi.’
9 Thus sayth the Lord, Deceiue not your selues, saying, The Caldeans shall surely depart from vs: for they shall not depart.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku ruɗe kanku, kuna tsammani, ‘Tabbatacce Babiloniyawa sun bar mu.’ Ba za su bari ba!
10 For though ye had smitten the whole hoste of the Caldeans that fight against you, and there remained but wounded men among them, yet should euery man rise vp in his tent, and burne this citie with fire.
Ko da a ce za ku ci dukan sojojin Babiloniyawan da suke yaƙi da ku har raunana ne kawai aka bari a tentunansu, za su fito su ƙone wannan birni.”
11 When the hoste of the Caldeans was broken vp from Ierusalem, because of Pharaohs armie,
Bayan sojojin Babiloniyawa suka janye daga Urushalima saboda sojojin Fir’auna,
12 Then Ieremiah went out of Ierusalem to goe into the land of Beniamin, separating himselfe thence from among the people.
sai Irmiya ya bar birnin don yă je yankin Benyamin ya sami rabon mallaka a cikin mutane a can.
13 And when hee was in the gate of Beniamin, there was a chiefe officer, whose name was Iriiah, the sonne of Shelemiah, the sonne of Hananiah, and he tooke Ieremiah the Prophet, saying, Thou fleest to the Caldeans.
Amma sa’ad da ya kai Ƙofar Benyamin, sai hafsa mai tsaro, wanda ake kira Iriya ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama shi ya kuma ce, “Kana gudu daga Babiloniyawa ne!”
14 Then sayde Ieremiah, That is false, I flee not to the Caldeans: but he would not heare him: so Iriiah tooke Ieremiah, and brought him to the princes.
Sai Irmiya ya ce, “Ba gaskiya ba ce, ba na gudu daga Babiloniyawa.” Amma Iriya bai saurare shi ba; a maimako, ya kama Irmiya ya kawo shi wurin fadawa.
15 Wherefore the princes were angry with Ieremiah, and smote him, and layde him in prison in the house of Iehonathan the scribe: for they had made that the prison.
Suka yi fushi da Irmiya suka sa aka yi masa dūka aka kuma jefa shi cikin kurkuku a gidan Yonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.
16 When Ieremiah was entred into the dungeon, and into the prisons, and had remained there a long time,
Aka sa Irmiya a can cikin kurkuku, inda ya kasance kwanaki masu yawa.
17 Then Zedekiah the King sent, and tooke him out, and the King asked him secretly in his house, and said, Is there any worde from the Lord? And Ieremiah sayd, Yea: for, sayd he, thou shalt be deliuered into the hand of the King of Babel.
Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
18 Moreouer, Ieremiah sayd vnto King Zedekiah, What haue I offended against thee, or against thy seruants, or against this people, that ye haue put me in prison?
Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
19 Where are nowe your prophets, which prophecied vnto you, saying, The King of Babel shall not come against you, nor against this land?
Ina annabawanka waɗanda suka yi maka annabci suna cewa, ‘Sarkin Babilon ba zai yaƙe ka ko wannan ƙasa ba’?
20 Therefore heare nowe, I pray thee, O my lorde the King: let my prayer be accepted before thee, that thou cause mee not to returne to the house of Iehonathan the scribe, least I die there.
Amma yanzu, ranka yă daɗe, sarkina, ka saurara. Bari in kawo kukata a gabanka. Kada ka mai da ni gidan Yonatan magatakarda, in ba haka zan mutu a can.”
21 Then Zedekiah the King commanded, that they should put Ieremiah in the court of the prison, and that they should giue him dayly a piece of bread out of the bakers streete vntill all the bread in the citie were eaten vp. Thus Ieremiah remained in the court of the prison.
Sarki Zedekiya ya yi umarni a ajiye Irmiya a sansanin matsara a kuma ba shi burodi daga titin masu gashin burodi kowace rana sai duka burodi a birnin ya ƙare. Saboda haka Irmiya ya zauna a sansanin matsara.

< Jeremiah 37 >