< Jeremiah 28 >

1 And that same yeere in the beginning of the reigne of Zedekiah King of Iudah in the fourth yeere, and in the fifth moneth Hananiah the sonne of Azur the prophet, which was of Gibeon, spake to mee in the House of the Lord in the presence of the Priestes, and of all the people, and said,
A wata na biyar na wannan shekara, shekara ta huɗu, a farkon sarautar Zedekiya sarkin Yahuda, sai annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibeyon, ya zo wurina a gidan Ubangiji a gaban firistoci da kuma dukan mutane,
2 Thus speaketh the Lord of hostes, the God of Israel, saying, I haue broken the yoke of the King of Babel.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan karya karkiyar sarkin Babilon.
3 Within two yeeres space I will bring into this place all the vessels of the Lords House, that Nebuchad-nezzar King of Babel tooke away from this place, and caried them into Babel.
Cikin shekaru biyu zan komo da dukan kayayyakin gidan Ubangiji da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe daga wannan wuri ya kai Babilon.
4 And I will bring againe to this place Ieconiah the sonne of Iehoiakim King of Iudah, with all them that were caried away captiue of Iudah, and went into Babel, saith the Lord: for I will breake the yoke of the King of Babel.
Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da kuma dukan sauran masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suka tafi Babilon,’ in ji Ubangiji, ‘gama zan karya karkiyar sarkin Babilon.’”
5 Then the Prophet Ieremiah saide vnto the Prophet Hananiah in the presence of ye Priests, and in the presence of all the people that stoode in the House of the Lord.
Sai annabi Irmiya ya amsa wa annabi Hananiya a gaban firistoci da kuma dukan mutane waɗanda suke tsaye a gidan Ubangiji.
6 Euen the Prophet Ieremiah sayde, So bee it: the Lord so doe, the Lord confirme thy words which thou hast prophecied to restore the vessels of the Lordes House, and al that is caried captiue, from Babel, into this place.
Ya ce, “Amin! Ubangiji yă sa yă zama haka! Ubangiji yă cika maganar da ka yi annabci ta wurin komo da kayayyakin gidan Ubangiji da kuma dukan masu zaman bauta zuwa wannan wuri daga Babilon.
7 But heare thou now this worde that I will speake in thine eares and in the eares of all the people.
Duk da haka, ka saurari abin da zan faɗa a kunnenka da kuma a kunnen duka mutane,
8 The Prophets that haue beene before mee and before thee in time past, prophecied against many countreyes, and against great kingdomes, of warre, and of plagues, and of pestilence.
Daga farko fari annabawan da suka riga ka da ni sun yi annabcin yaƙi, masifa da annoba a kan ƙasashe masu yawa da kuma manyan mulkoki.
9 And the Prophet which prophecieth of peace, when the word of the Prophet shall come to passe, then shall the Prophet be knowen that the Lord hath truely sent him.
Amma annabin da ya yi annabcin salama shi za a ɗauka a matsayin wanda Ubangiji ya aika in har abin da ya furta ya zama gaskiya.”
10 Then Hananiah the Prophet tooke the yoke from the Prophet Ieremiahs necke, and brake it.
Sai annabi Hananiya ya cire karkiya daga wuyar annabi Irmiya ya karya ta,
11 And Hananiah spake in the presence of all the people, saying, Thus saith the Lord, Euen so will I breake the yoke of Nebuchad-nezzar King of Babel, from the necke of al nations within the space of two yeres: and the Prophet Ieremiah went his way.
ya ce a gaban dukan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘A haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar sarkin Babilon daga wuyan dukan al’ummai a cikin shekaru biyu.’” Da wannan, annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.
12 Then the word of the Lord came vnto Ieremiah the Prophet, (after that Hananiah the Prophet had broken the yoke from the necke of the Prophet Ieremiah) saying,
Ba a daɗe ba bayan annabi Hananiya ya karya karkiya daga wuyan annabi Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
13 Go, and tell Hananiah, saying, Thus sayth the Lord, Thou hast broken the yokes of wood, but thou shalt make for them yokes of yron.
“Je ka faɗa wa Hananiya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka karya karkiyar katako, amma a wurinsa za ka sami karkiyar ƙarfe.
14 For thus saith the Lord of hostes the God of Israel, I haue put a yoke of yron vpon the necke of all these nations, that they may serue Nebuchad-nezzar King of Babel: for they shall serue him, and I haue giuen him the beasts of the fielde also.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’”
15 Then sayd the Prophet Ieremiah vnto the Prophet Hananiah, Heare nowe Hananiah, the Lord hath not sent thee, but thou makest this people to trust in a lye.
Sa’an nan annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka saurara, Hananiya! Ubangiji bai aike ka ba, duk da haka ka lallashe wannan al’umma su dogara ga ƙarya.
16 Therefore thus saith the Lord, Beholde, I will cast thee from of the earth: this yeere thou shalt die, because thou hast spoken rebelliously against the Lord.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Ina shirin kawar da kai daga fuskar duniya. A wannan shekara za ka mutu, domin ka yi wa’azin tawaye a kan Ubangiji.’”
17 So Hananiah the Prophet died the same yeere in the seuenth moneth.
A wata na bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.

< Jeremiah 28 >