< Jeremiah 14 >

1 The worde of the Lord that came vnto Ieremiah, concerning the dearth.
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya game da fări cewa,
2 Iudah hath mourned, and the gates thereof are desolate, they haue bene brought to heauinesse vnto the grounde, and the cry of Ierusalem goeth vp.
“Yahuda tana makoki biranenta suna fama; suna kuka saboda ƙasar, kuka kuma tana tasowa daga Urushalima.
3 And their nobles haue sent their inferiours to the water, who came to the welles, and founde no water: they returned with their vessels empty: they were ashamed and confounded, and couered their heads.
Manyan mutane suna aika bayinsu su ɗebo ruwa a maɓulɓulai amma babu ruwa. Suka dawo da tulunansu haka nan; da kunya da kuma ƙasƙanci, da kawunansu a rufe.
4 For the grounde was destroyed, because there was no rayne in the earth: the plowmen were ashamed, and couered their heads.
Ƙasa ta tsattsage saboda babu ruwan sama a ƙasar; manoma sun sha kunya suka kuma rufe kawunansu.
5 Yea, the hinde also calued in the fielde, and forsooke it, because there was no grasse.
Har barewa a kurmi ma ta gudu ta bar’ya’yan da ta haihu sababbi saboda babu ciyawa.
6 And the wilde asses did stande in the hygh places, and drew in their winde like dragons their eyes did faile, because there was no grasse.
Jakan jeji suna tsaye a kan tuddai suna haki kamar diloli; idanunsu sun kāsa gani saboda rashin makiyaya.”
7 O Lord, though our iniquities testifie against vs, deale with vs according to thy name: for our rebellions are many, we sinned against thee.
Ko da yake zunubanmu suna ba da shaida a kanmu, Ya Ubangiji, ka yi wani abu saboda sunanka. Gama jan bayanmu ya yi yawa; mun yi maka zunubi.
8 O the hope of Israel, the sauiour thereof in the time of trouble, why art thou as a strager in ye land, as one that passeth by to tary for a night?
Ya kai, Sa Zuciyar Isra’ila, Mai Cetonsa a lokutan wahala, me ya sa kake yi kamar baƙo a ƙasar, kamar matafiyi wanda yake shirya wuri don yă kwana gari ya waye ya wuce?
9 Why art thou as a man astonied, and as a strong man that cannot helpe? yet thou, O Lord, art in the middes of vs, and thy Name is called vpon vs: forsake vs not.
Me ya sa kake yi kamar mutumin da aka far masa kwasam ba zato, kamar jarumi marar ƙarfin ceto? Kana a cikinmu, ya Ubangiji, da sunanka ake kiranmu; kada ka yashe mu!
10 Thus saith the Lord vnto this people, Thus haue they delited to wander: they haue not refrained their feete, therefore the Lord hath no delight in them: but he will now remember their iniquitie, and visite their sinnes.
Ga abin da Ubangiji ya ce game da wannan mutane, “Suna son yawace-yawace ƙwarai; ba sa hana ƙafafunsu yawo. Saboda haka Ubangiji bai yarda da su ba; yanzu zai tuna da muguntarsu zai kuma hukunta su saboda zunubansu.”
11 Then sayd the Lord vnto me, Thou shalt not pray to do this people good.
Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu’a domin zaman lafiyar mutanen nan.
12 When they fast, I will not heare their cry, and when they offer burnt offering, and an oblation, I will not accept them: but I will consume them by the sworde, and by the famine and by the pestilence.
Ko da yake suna azumi, ba zan saurari kukansu ba, ko da yake suna miƙa hadayun ƙonawa da hadayun gari, ba zan yarda da su ba. A maimako zan hallaka su da takobi, yunwa da annoba.”
13 Then answered I, Ah Lord God, beholde, the prophets say vnto them, Ye shall not see the sworde, neither shall famine come vpon you, but I wil giue you assured peace in this place.
Amma na ce, “A, Ubangiji Mai Iko Duka, annabawa sun riƙa ce musu, ‘Ba za ku ga takobi ko ku yi fama da yunwa ba. A maimako, zan ba ku madawwamiyar salama.’”
14 Then the Lord said vnto me, The prophets prophecie lyes in my Name: I haue not sent them, neither did I command them, neither spake I vnto them, but they prophecie vnto you a false vision, and diuination, and vanitie, and deceitfulnes of their owne heart.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Annabawa suna ta annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba, ban kuma naɗa su ba, ban yi musu magana ba. Suna muku annabci wahayin ƙarya, suna muku duba marar amfani, suna bautar gumaka suna kuma bayyana tunanin kansu ne.
15 Therefore thus saith the Lord, Concerning the prophets that prophecie in my Name, whom I haue not sent, yet they say, Sworde and famine shall not be in this land, by sword and famine shall those prophets be consumed.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce game da annabawan da suke annabci da sunana. Ban aike su ba, duk da haka suna cewa, ‘Babu takobi ko yunwar da zai taɓa wannan ƙasa.’ Waɗannan annabawa takobi da yunwa za su hallaka su.
16 And the people to whome these prophets doe prophecie, shalbe cast out in the streetes of Ierusalem, because of the famine, and the sword, and there shall be none to bury them, both they, and their wiues, and their sonnes, and their daughters: for I wil powre their wickednes vpon them.
Mutanen da suke musu annabcin kuwa za a kore su zuwa titunan Urushalima saboda yunwa da kuma takobi. Babu wanda zai binne su, ko ya binne matansu, ko’ya’yansu maza da mata. Zan aukar musu da masifar da ya dace da su.
17 Therefore thou shalt say this worde vnto them, Let mine eyes drop downe teares night and day without ceasing: for the virgine daughter of my people is destroyed with a great destruction, and with a sore grieuous plague.
“Ka yi musu wannan magana, “‘Bari idanuna su yi ta zub da hawaye dare da rana kada su daina; saboda’yata budurwa, mutanena, sun sha wahalar babban rauni, an yi musu bugu mai ragargazawa.
18 For if I go into the field, behold the slaine with the sworde: and if I enter into the citie, behold them that are sicke for hunger also: moreouer the Prophet also and the Priest go a wandring into a land that they know not.
In na shiga cikin ƙasar, na ga waɗanda takobi ya kashe; in na shiga cikin birni, na ga waɗanda suke fama da yunwa. Da Annabi da firist duk sun tafi ƙasar da ba su sani ba.’”
19 Hast thou vtterly reiected Iudah, or hath thy soule abhorred Zion? why hast thou smitten vs, that we cannot be healed? Wee looked for peace, and there is no good, and for the time of health, and behold trouble.
Ka ƙi Yahuda ɗungum ke nan? Kana ƙyamar Sihiyona ne? Me ya sa ka buge mu don kada mu warke? Mun sa zuciya ga salama babu abin alherin da ya zo, mun sa rai ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
20 We acknowledge, O Lord, our wickednesse and the iniquitie of our fathers: for we haue sinned against thee.
Ya Ubangiji, mun gane da muguntarmu da kuma laifin kakanninmu; tabbatacce mun yi maka zunubi.
21 Doe not abhorre vs: for thy Names sake cast not downe the throne of thy glory: remember and breake not thy couenant with vs.
Saboda sunanka kada ka ƙi mu; kada ka ƙasƙantar da kursiyoyinka mai ɗaukaka. Ka tuna da alkawarinka da mu kada ka tā da shi.
22 Are there any among the vanities of the Gentiles, that can giue raine? or can the heauens giue showres? is it not thou, O Lord our God? therefore we will waite vpon thee: for thou hast made all these things.
Akwai wani daga cikin gumaka marasa amfani na al’ummai da ya kawo ruwan sama? Sararin sama kansu sukan yi yayyafi? A’a, kai ne, ya Ubangiji Allahnmu. Saboda haka sa zuciyarmu tana a kanka, gama kai ne kake yi wannan duka.

< Jeremiah 14 >