< Isaiah 9 >

1 Yet the darkenesse shall not be according to the affliction that it had when at the first hee touched lightly the land of Zebulun and the land of Naphtali, nor afteward when he was more grieuous by the way of the sea beyond Iorden in Galile of the Gentiles.
Duk da haka, babu sauran baƙin ciki ga waɗanda suke shan azaba. Dā ya ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zebulun da ƙasar Naftali, amma nan gaba zai girmama Galili na Al’ummai, ta hanyar teku wadda take ta Urdun.
2 The people that walked in darkenes haue seene a great light: they that dwelled in the land of the shadowe of death, vpon them hath the light shined.
Mutanen da suke tafiya cikin duhu sun ga babban haske; a kan waɗanda suke zama a ƙasar inuwar mutuwa haske ya haskaka.
3 Thou hast multiplied the nation, and not increased their ioye: they haue reioyced before thee according to the ioye in haruest, and as men reioyce when they deuide a spoyle.
Ka fadada al’umma ka kuma ƙara farin cikinsu; suna farin ciki a gabanka yadda mutane sukan yi murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane sukan yi farin ciki sa’ad da suke raba ganima.
4 For the yoke of their burthen, and the staffe of their shoulder and the rod of their oppressour hast thou broken as in the day of Midian.
Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.
5 Surely euery battell of the warriour is with noyse, and with tumbling of garments in blood: but this shall be with burning and deuouring of fire.
Kowane takalmin jarumin da aka yi amfani da shi a yaƙi da kuma kowane rigar da ka naɗe cikin jini zai kasance an ƙone shi zai kuma zama abin hura wuta.
6 For vnto vs a childe is borne, and vnto vs a Sonne is giuen: and the gouernement is vpon his shoulder, and he shall call his name Wonderfull, Counseller, The mightie God, The euerlasting Father, The prince of peace,
Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban Madawwami, Sarkin Salama.
7 The increase of his gouernement and peace shall haue none end: he shall sit vpon the throne of Dauid, and vpon his kingdome, to order it, and to stablish it with iudgement and with iustice, from hencefoorth, euen for euer: the zeale of the Lord of hostes will performe this.
Game da girmar gwamnatinsa da salama babu iyaka. Zai gāji sarki Dawuda, yă yi mulki a matsayinsa, zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Maɗaukaki ne ya yi niyyar aikata wannan duka.
8 The Lord hath sent a worde into Iaakob, and it hath lighted vpon Israel.
Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
9 And all the people shall knowe, euen Ephraim, and the inhabitant of Samaria, that say in the pride and presumption of the heart,
Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
10 The brickes are fallen, but we will build it with hewen stones: the wilde figge trees are cut downe, but we will change them into ceders.
“Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”
11 Neuerthelesse the Lord will raise vp the aduersaries of Rezin against him, and ioyne his enemies together.
Amma Ubangiji ya ƙarfafa maƙiyan Rezin gāba da su ya kuma ingiza abokan gāba.
12 Aram before and the Philistims behinde, and they shall deuoure Israel with open mouth: yet for all this his wrath is not turned away, but his hand is stretched out still.
Arameyawa daga gabas da Filistiyawa daga yamma sun cinye Isra’ila da buɗaɗɗen baki. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
13 For the people turneth not vnto him that smiteth them, neither doe they seeke the Lord of hostes.
Amma mutanen ba su juyo wurin wanda ya buge su ba, balle su nemi Ubangiji Maɗaukaki.
14 Therefore will the Lord cut off from Israel head and taile, branche and rush in one day.
Saboda haka Ubangiji zai yanke Isra’ila kai da wutsiya, da reshen dabino da iwa a rana guda;
15 The ancient and the honorable man, he is the head: and the prophet that teacheth lies, he is the taile.
dattawa da manyan mutane su ne kai, annabawa waɗanda suke koyar da ƙarairayi su ne wutsiya.
16 For the leaders of the people cause them to erre: and they that are led by them are deuoured.
Waɗanda suke jagorar wannan mutane suna ɓad da su, su ne waɗanda ake jagora aka sa suka kauce.
17 Therefore shall the Lord haue no pleasure in their yong men, neither will he haue compassion of their fatherlesse and of their widowes: for euery one is an hypocrite and wicked, and euery mouth speaketh follie: yet for all this his wrath is not turned away, but his hand is stretched out stil.
Saboda haka Ubangiji ba zai ji daɗin matasa ba, ba kuwa zai ji tausayin marayu da gwauraye ba, gama kowa marar sanin Allah ne da kuma mugu, kowane baki yana faɗin mugayen maganganu. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
18 For wickednesse burneth as a fire: it deuoureth the briers and the thornes and will kindle in the thicke places of the forest: and they shall mount vp like the lifting vp of smoke.
Tabbatacce mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya, ta sa wuta a jeji mai itatuwa masu yawa, don yă yi murtuke hayaƙi har zuwa sama.
19 By the wrath of the Lord of hostes shall the land be darkened, and the people shall be as the meate of ye fire: no man shall spare his brother.
Ta wurin fushin Ubangiji Maɗaukaki ƙasar za tă ci wuta mutane kuma za su zama abin hura wutar, babu wanda zai ji tausayin ɗan’uwansa.
20 And he shall snatch at the right hand, and be hungrie: and he shall eate on the left hand, and shall not be satisfied: euery one shall eate ye flesh of his owne arme.
A dama za su ci, amma su ci gaba da jin yunwa; a hagu za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Kowa zai mai da naman’ya’yansa abinci.
21 Manasseh, Ephraim: and Ephraim Manasseh, and they both shall be against Iudah yet for all this his wrath is not turned away, but his hand is stretched out still.
Manasse zai mai da Efraim abinci, Efraim kuma yă cinye Manasse; tare za su yi gāba da Yahuda. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.

< Isaiah 9 >