< Isaiah 34 >

1 Come neere, ye nations and heare, and hearken, ye people: let the earth heare and all that is therein, the world and al that proceedeth thereof.
Ku zo kusa, ku al’ummai, ku kuwa saurara ku kasa kunne, ku mutane! Bari duniya ta ji, da kuma dukan abin da yake cikinta, duniya, da dukan abin da yake fitowa daga gare ta!
2 For the indignation of the Lord is vpon all nations, and his wrath vpon all their armies: hee hath destroyed them and deliuered them to the slaughter.
Ubangiji yana fushi da dukan al’ummai; hasalarsa tana a kan mayaƙansu. Zai hallaka su tas, zai ba da su a karkashe.
3 And their slaine shalbe cast out, and their stincke shall come vp out of their bodies, and the mountaines shalbe melted with their blood.
Za a jefar da waɗanda aka kashe gawawwakinsu za su yi wari; duwatsu za su jiƙu da jininsu.
4 And all the hoste of heauen shalbe dissolued, and the heauens shall be folden like a booke: and all their hostes shall fall as the leafe falleth from the vine, and as it falleth from the figtree.
Za a tumɓuke dukan taurarin sammai za a kuma nannaɗe sararin sama kamar littafi; dukan rundunar sama za su fāffāɗi kamar ganyayen da suka yanƙwane daga kuringa, kamar’ya’yan ɓauren da suka bushe daga itacen ɓaure.
5 For my sword shalbe drunken in the heauen: beholde, it shall come downe vpon Edom, euen vpon the people of my curse to iudgement.
Takobina ya sha zararsa a cikin sammai; duba, ya sauko cikin hukunci a kan Edom, mutanen da zan hallaka tas.
6 The sword of the Lord is filled with blood: it is made fat with the fat and with the blood of the lambes and the goates, with the fat of the kidneis of the rams: for the Lord hath a sacrifice in Bozrah, and a great slaughter in the land of Edom.
Takobin Ubangiji ya jiƙu da jini, ya rufu da kitse, jinin raguna da na awaki, kitse daga ƙodar raguna. Gama Ubangiji ya yi hadayar Bozra da kuma babban kisa a Edom.
7 And the vnicorne shall come downe with them and the heiffers with the bulles, and their lande shalbe drunken with blood, and their dust made fat with fatnesse.
Babban bijimin jeji zai fāɗi tare da su, maruƙan bijimi da manyan bijimai. Ƙasarsu za tă cika da jini, ƙura kuma zai cika da kitse.
8 For it is the day of the Lordes vengeance, and the yeere of recompence for the iudgement of Zion.
Gama Ubangiji yana da ranar ɗaukar fansa, shekarar ramuwa, don biya wa Sihiyona bukata.
9 And the riuers thereof shall be turned into pitche, and the dust thereof into brimstone, and the land thereof shalbe burning pitch.
Za a mai da rafuffukan Edom rami, ƙurarta za tă zama kibiritun farar wuta; ƙasarta za tă zama rami mai ƙuna!
10 It shall not be quenched night nor day: the smoke thereof shall goe vp euermore: it shall be desolate from generation to generation: none shall passe through it for euer.
Ba za a kashe ta ba dare da rana; hayaƙinta za tă yi ta tashi har abada. Daga tsara zuwa tsara za tă zama kango; babu wani da zai ƙara wucewa ta wurin.
11 But the pelicane and the hedgehog shall possesse it, and the great owle, and the rauen shall dwel in it, and he shall stretch out vpon it the line of vanitie, and the stones of emptinesse.
Mujiyar hamada da mujiya mai kuka za su mallake ta; babban mujiya da hankaka za su yi sheƙa a can. Allah zai miƙe a kan Edom magwajin bala’i da ma’aunin kango.
12 The nobles thereof shall call to the kingdome, and there shalbe none, and all the princes thereof shalbe as nothing.
Sarakunanta ba za su kasance da wani abin da ake kira masarauta ba, dukan sarakunanta za su ɓace.
13 And it shall bring foorth thornes in the palaces thereof, nettles and thistles in the strong holdes thereof, and it shall be an habitation for dragons, and a court for ostriches.
Ƙayayuwa za su mamaye fadodinta ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya za su cika kagaranta. Za tă zama mazaunin diloli da gida don mujiyoyi.
14 There shall meete also Ziim and Iim, and the Satyre shall cry to his fellow, and the shricheowle shall rest there, and shall finde for her selfe a quiet dwelling.
Halittun hamada za su sadu da kuraye, awakin jeji za su yi ta kiran juna; a can halittun dare su ma za su huta su kuma nemi wurin hutu wa kansu.
15 There shall the owle make her nest, and laye, and hatche, and gather them vnder her shadowe: there shall the vultures also bee gathered, euery one with her make.
Mujiya za tă yi sheƙa a can ta zuba ƙwai; za tă ƙyanƙyashe su, ta kuma kula da’ya’yanta a inuwar fikafikanta; a can kuma shirwa za su taru, kowa da abokinsa.
16 Seeke in the booke of the Lord, and reade: none of these shall fayle, none shall want her make: for his mouth hath commanded, and his very Spirit hath gathered them.
Duba a cikin littafin Ubangiji ka kuma karanta. Babu wani a cikin waɗannan da ya ɓace, babu ko ɗaya da ba ta da abokiya. Gama bakinsa ne ya ba da umarni, Ruhunsa kuma zai tara su wuri ɗaya.
17 And he hath cast the lot for them, and his hand hath deuided it vnto them by line: they shall possesse it for euer: from generation to generation shall they dwell in it.
Ya ba su rabonsu; hannunsa ya rarraba musu ta wurin awo. Za su mallake ta har abada su kuma zauna a can daga tsara zuwa tsara.

< Isaiah 34 >