< Isaiah 17 >

1 The burden of Damascus. Beholde, Damascus is taken away from being a citie, for it shall be a ruinous heape.
Abin da Allah ya faɗa game da Damaskus. “Duba, Damaskus ba za tă ƙara zama birni ba amma za tă zama tsibin juji.
2 The cities of Aroer shall be forsaken: they shall be for the flockes: for they shall lye there, and none shall make them afraide.
Za a watse a bar biranen Arower a bar wa tumaki da shanu, waɗanda za su kwanta, ba tare da wani wanda zai tsorata su ba.
3 The munition also shall cease from Ephraim, and the kingdome from Damascus, and the remnant of Aram shall be as the glory of the children of Israel, sayeth the Lord of hostes.
Birni mai katanga za tă ɓace daga Efraim, ikon sarauta kuma daga Damaskus; raguwar Aram za tă zama kamar darajar Isra’ila,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
4 And in that day the glorie of Iaakob shall be impouerished, and the fatnes of his flesh shalbe made leane.
“A wannan rana ɗaukakar Yaƙub za tă ƙare; kitsen jikinsa zai lalace.
5 And it shalbe as when the haruest man gathereth the corne, and reapeth the eares with his arme, and he shall be as he that gathereth the eares in the valley of Rephaim.
Zai zama kamar sa’ad da mai girbi ya tara hatsin da yake tsaye ya kuma girbe hatsin da hannunsa kamar sa’ad da mutum ya yi kala kawunan hatsi a Kwarin Refayim.
6 Yet a gathering of grapes shall be left in it, as the shaking of an oliue tree, two or three beries are in the top of the vpmost boughes, and foure or fiue in the hie branches of the fruite thereof, sayeth the Lord God of Israel.
Duk da haka waɗansu kala za su ragu, sai ka ce sa’ad da an karkaɗe itace zaitun, aka bar’ya’yan zaitun biyu ko uku a can ƙwanƙolin rassan, ko kuma aka bar huɗu ko biyar a rassa na gefe na itace mai’ya’ya,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila.
7 At that day shall a man looke to his maker, and his eyes shall looke to the holy one of Israel.
A wannan rana mutane za su nemi Mahaliccinsu su kuma juye idanunsu ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
8 And hee shall not looke to the altars, the workes of his owne hands, neither shall he looke to those thinges, which his owne fingers haue made, as groues and images.
Ba za su dubi bagade ba, waɗanda suke aikin hannuwansu, ba za su kuma kula da ginshiƙan Ashera ba da kuma bagadan turaren da yatsotsinsu suka yi.
9 In that day shall the cities of their strength be as the forsaking of boughes and branches, which they did forsake, because of the children of Israel, and there shall be desolation.
A wannan rana biranensu masu ƙarfi, waɗanda suka bari saboda Isra’ilawa, za su zama kamar wuraren da aka ƙyale suka zama kufai a jeji. Za su kuma zama kango.
10 Because thou hast forgotten the God of thy saluation, and hast not remembred the God of thy strength, therefore shalt thou set pleasant plantes, and shalt graffe strange vine branches:
Kun manta da Allah Mai Cetonku; ba ku tuna da Dutse, kagararku ba. Saboda haka, ko da yake kun fita ku shuka tsire-tsire mafi kyau kuka kuma shuka inabin da aka sayo daga waje,
11 In the day shalt thou make thy plant to growe, and in the morning shalt thou make thy seede to florish: but the haruest shall be gone in the day of possession, and there shalbe desperate sorrowe.
ko da yake a ranar kun shuka su, kuka sa su yi girma, da safe kuma sa’ad da kuka shuka su, kuka sa suka yi toho suka yi fure, duk da haka girbin ba zai zama kome ba a ranar cuta da zafin da ba ta da magani.
12 Ah, the multitude of many people, they shall make a sounde like the noyse of the sea: for the noyse of the people shall make a sounde like the noyse of mightie waters.
Kash, ga hayaniyar al’ummai masu yawa suna hayaniya kamar rurin teku! Kash, ga fushin mutane suna ruri kamar rugugi kamar manyan ruwaye!
13 The people shall make a sounde like the noise of many waters: but God shall rebuke them, and they shall flee farre off, and shalbe chased as the chaffe of the mountaines before the winde, and as a rolling thing before the whirlewinde.
Ko da yake mutane suna ruri kamar sukuwar raƙuman ruwa, sa’ad da ya tsawata musu za su gudu can da nisa, aka kore su kamar yayinda iska ya hura a kan tuddai, kamar tattake kuma a cikin guguwa.
14 And loe, in the euening there is trouble: but afore the morning it is gone. This is the portion of them that spoyle vs, and the lot of them that robbe vs.
Da yamma, sai razana ba tsammani! Kafin safiya, duk sun ɓace! Wannan ne rabon waɗanda suka washe mu, rabon waɗanda suka yi mana ƙwace.

< Isaiah 17 >