< Isaiah 16 >

1 Send yee a lambe to the ruler of the worlde from the rocke of the wildernesse, vnto the mountaine of the daughter Zion.
Ku aiko da raguna a matsayin haraji ga mai mulkin ƙasar, daga Sela a hamada, zuwa dutsen Diyar Sihiyona.
2 For it shall be as a birde that flieth, and a nest forsaken: the daughters of Moab shall be at the foordes of Arnon.
Kamar tsuntsaye masu firiya da aka kora daga sheƙa, haka matan Mowab suke a kogunan Arnon.
3 Gather a cousel, execute iudgement: make thy shadowe as the night in the midday: hide them that are chased out: bewray not him that is fled.
“Ku ba mu shawara, ku yanke shawara. Ku mai da inuwarku kamar dare, a tsakar rana. Ku ɓoye masu gudun hijira, kada ku bashe masu neman mafaka.
4 Let my banished dwell with thee: Moab be thou their couert from the face of the destroyer: for the extortioner shall ende: the destroyer shalbe consumed, and the oppressour shall cease out of the land.
Ku bar Mowabawa masu gudun hijira su zauna tare da ku; ku zama mafakarsu daga mai neman hallaka su.” Mai danniya zai zo ga ƙarshe hallaka kuma za tă daina; masu lalatar da ƙasa za su kare
5 And in mercy shall the throne be prepared, and hee shall sit vpon it in stedfastnesse, in the tabernacle of Dauid, iudging, and seeking iudgement, and hasting iustice.
Da ƙauna za a kafa kursiyi; da aminci mutum zai zauna a kansa, wani daga gidan Dawuda, wani wanda ta shari’antawa yakan nuna gaskiya ya hanzarta yin adalci.
6 We haue heard of the pride of Moab, (he is very proud) euen his pride, and his arrogancie, and his indignation, but his lies shall not be so.
Mun ji fariyar Mowab, mun ji yawan fariyarta da girmankanta, fariyarta da reninta, amma taƙamarsu ta banza ce.
7 Therefore shall Moab howle vnto Moab: euery one shall howle: for the foundations of Kirhareseth shall ye mourne, yet they shalbe striken.
Saboda haka Mowabawa za su yi kuka mai zafi, za su yi kuka mai zafi tare saboda Mowab. Ku yi makoki ku kuma yi baƙin ciki saboda ƙosai da kuka riƙa ci a Kir Hareset.
8 For ye vineyards of Heshbon are cut downe, and the vine of Sibmah: the lordes of the heathen haue broken the principal vines thereof: they are come vnto Iaazer: they wandred in the wildernesse: her goodly branches stretched out them selues, and went ouer the sea.
Gonakin Heshbon sun bushe, inabin Sibma ma haka. Masu mulkin al’ummai sun tattake inabi mafi kyau, waɗanda suka taɓa yaɗuwa zuwa Yazer suka bazu ta wajen hamada. Tohonsu sun buɗu suka kai har teku.
9 Therefore will I weepe with the weeping of Iaazer, and of the vine of Sibmah, O Heshbon: and Elealeh, I will make thee drunke with my teares, because vpon thy sommer fruits, and vpon thy haruest a showting is fallen.
Saboda haka na yi kuka, yadda Yazer take kuka, saboda inabin Sibma. Ya Heshbon, ya Eleyale, na cika ku da hawaye! Sowa ta murna a kanku saboda’ya’yan itatuwanku da suka nuna da kuma girbinku sun ɓace.
10 And gladnes is taken away, and ioy out of the plentifull fielde: and in the vineyardes shall be no singing nor shouting for ioy: the treader shall not tread wine in the wine presses: I haue caused the reioycing to cease.
An ɗauke farin ciki da murna daga gonakin itatuwa masu’ya’ya; babu wanda yake rerawa ko yake sowa a cikin gonakin inabi; babu wanda yake matsin ruwan inabi a wuraren matsi, gama na kawo ƙarshen yin sowa.
11 Wherefore, my bowels shall sounde like an harpe for Moab, and mine inwarde partes for Ker-haresh.
Zuciyata tana makoki saboda Mowab kamar garaya, na yi baƙin ciki saboda Kir Hareset.
12 And when it shall appeare that Moab shall be wearie of his hie places, then shall hee come to his temple to praie, but he shall not preuaile.
Sa’ad Mowab ta bayyana a masujadar bisa tudu, tana gajiyar da kanta ne kawai; sa’ad da ta tafi wurin tsafinta don tă yi addu’a, babu wani amfani.
13 This is the word that the Lord hath spoken against Moab since that time.
Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya riga ya yi game da Mowab.
14 And nowe the Lord hath spoken, saying, In three yeres, as the yeeres of a hireling, and the glorie of Moab shall be contemned in all the great multitude, and the remnant shalbe very small and feeble.
Amma yanzu Ubangiji ya ce, “Cikin shekara uku, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, haka za a mai da daraja da kuma dukan yawan mutanen Mowab abin reni, daga ɗumbun mutanenta,’yan kaɗan ne kaɗai za su ragu, za su kuma zama marasa ƙarfi.”

< Isaiah 16 >