< Isaiah 14 >

1 For the Lord wil haue compassion of Iaakob, and wil yet chuse Israel, and cause them to rest in their owne lande: and the stranger shall ioyne him selfe vnto them, and they shall cleaue to the house of Iaakob.
Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
2 And the people shall receiue them and bring them to their owne place, and the house of Israel shall possesse them in the land of the Lord, for seruants and handmaids: and they shall take them prisoners, whose captiues they were, and haue rule ouer their oppressours.
Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
3 And in that day when the Lord shall giue thee rest from thy sorrow, and from thy feare, and from the sore bodage, wherein thou didest serue,
A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
4 Then shalt thou take vp this prouerbe against the King of Babel, and say, Howe hath the oppressor ceased? and the gold thirsty Babel rested?
za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
5 The Lord hath broken the rodde of the wicked, and the scepter of the rulers:
Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
6 Which smote the people in anger with a continuall plague, and ruled the nations in wrath: if any were persecuted, he did not let.
wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
7 The whole worlde is at rest and is quiet: they sing for ioye.
Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
8 Also the firre trees reioyced of thee, and the cedars of Lebanon, saying, Since thou art laid downe, no hewer came vp against vs.
Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
9 Hel beneath is mooued for thee to meete thee at thy comming, raising vp the deade for thee, euen all the princes of the earth, and hath raised from their thrones all the Kinges of the nations. (Sheol h7585)
Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol h7585)
10 All they shall crie, and saie vnto thee, Art thou become weake also as we? art thou become like vnto vs?
Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
11 Thy pompe is brought downe to ye graue, and the sounde of thy violes: the worme is spred vnder thee, and the wormes couer thee. (Sheol h7585)
An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol h7585)
12 How art thou fallen from heauen, O Lucifer, sonne of the morning? and cutte downe to the grounde, which didest cast lottes vpon the nations?
Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
13 Yet thou saidest in thine heart, I will ascende into heauen, and exalt my throne aboue beside the starres of God: I will sitte also vpon the mount of the Congregation in the sides of the North.
Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
14 I wil ascend aboue ye height of the cloudes, and I will be like the most high.
Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
15 But thou shalt bee brought downe to the graue, to the sides of the pit. (Sheol h7585)
Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol h7585)
16 They that see thee, shall looke vpon thee and consider thee, saying, Is this the man that made the earth to tremble, and that did shake the kingdomes?
Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
17 He made the worlde as a wildernesse, and destroied the cities thereof, and opened not the house of his prisoners.
mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
18 All the Kings of the nations, euen they all sleepe in glorie, euery one in his owne house.
Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
19 But thou art cast out of thy graue like an abominable branch: like the raiment of those that are slaine, and thrust thorowe with a sword, which goe downe to the stones of the pit, as a carkeise troden vnder feete.
Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
20 Thou shalt not be ioyned with them in the graue, because thou hast destroied thine owne lande, and slaine thy people: the seede of the wicked shall not be renoumed for euer.
ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
21 Prepare a slaughter for his children, for the iniquitie of their fathers: let them not rise vp nor possesse the land, nor fil the face of the world with enemies.
A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
22 For I wil rise vp against them (sayth the Lord of hostes) and will cut off from Babel the name and the remnant and the sonne, and the nephew, sayth the Lord:
“Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
23 And I wil make it a possession to ye hedgehogge, and pooles of water, and I will sweepe it with the besome of destruction, sayeth the Lord of hostes.
“Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
24 The Lord of hostes hath sworne, saying, Surely like as I haue purposed, so shall it come to passe, and as I haue consulted, it shall stand:
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
25 That I will breake to pieces Asshur in my land, and vpon my mountaines will I treade him vnder foote: so that his yoke shall depart from them, and his burden shall be taken from off their shoulder.
Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
26 This is the counsell that is consulted vpon the whole worlde, and this is the hande stretched out ouer all the nations,
Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
27 Because the Lord of hostes hath determined it, and who shall disanull it? and his hande is stretched out, and who shall turne it away?
Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
28 In the yeere that King Ahaz died, was this burden.
Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
29 Reioyce not, (thou whole Palestina) because the rod of him that did beat thee, is broken for out of the serpents roote shall come forth a cockatrise, and the fruit therof shalbe a firy flying serpent.
Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
30 For the first borne of the poore shall be fed, and the needie shall lie downe in safetie: and I will kill thy roote with famine, and it shall slay thy remnant.
Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
31 Howle, O gate, crie, O citie: thou whole lande of Palestina art dissolued, for there shall come from the North a smoke, and none shalbe alone, at his time appointed.
Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
32 What shall then one answere the messengers of the Gentiles? That the Lord hath stablished Zion, and the poore of his people shall trust in it.
Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”

< Isaiah 14 >